Connect with us

Labarai

An cimma matsaya tsakanin ‘yan kasuwa da gwamnati kan wutar Solar

Published

on

Kwamishinan kasuwanci masana’antu da ma’adanai na jihar Kano, Alhaji Mahmud Muhammad Hantsi, ya bayyana cewa sabanin da aka samu a baya tsakanin ‘yan kasuwar Sabon Gari da shugabanin kasuwar kan na’ura mai amfani da hasken rana izuwa yanzu an samu dai-daito a tsakani.

Alhaji Mahmud Hantsi, ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai da hukumar ta gudanar a ranar Litinin,

Yayin zaman taron na sulhu

Ya ce” Gwamnati ta samar da na’urar mai amfani da hasken rana Solar ne ga ‘yan kasuwar ta Sabon gari domin kara samar da tsaro da kuma kare rayukan al’umma a cikin kasuwar. Kuma a yanzu haka mun samarwa da ‘yan kasuwar tsari na zamanantar da kasuwancin su a shafukan internet wanda kowan ne dan kasuwa zai iya yin rijistar kasuwancin sa ta shafukan”. Inji Hantsi.

Da yake nasa jawabin a yayin taron Shugaban kasuwar Sabon Gari, Alhaji Uba Zubairu Yakasai, cewa ya yi “Mun samar da na’urar SolaR a kasuwar ne da sanin gwamnatin jihar Kano”. A cewar Uba Zubairu,

Wakilin mu Hassan Mamuda Ya’u ya rawaito cewa, Kwamishinan Kasuwancin Alhaji Mahmuda Muhammad Hantsi, ya kuma shawarci ‘yan kasuwa da cewar, matukar su ka ga wani bakon abu da basu gamsu da shi ba daga lafiyar ‘yan kasuwar su sanar da manyan kasuwanni domin gudun kamuwa da cutar Corona Virus.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending