Connect with us

Labarai

Kano: Wata mata ta rotse kan facalar ta da tabarya

Published

on

Wata mata an yi zargin ta rotse kan facalar ta da tabarya, ta kuma kada ita a kan yaron cikin da ta dauke da shi, wadanda ke zaune a gida daya a unguwar Birget PRP a jihar Kano.

An yi zargin dai facalolin sabani ne ya gifta a tsakaninsu, inda matar kanin Khadija Isma’il, ta yi amfani da tabarya ta rotse kan matar wan mijin nata mai suna Jamila Shehu.

Bayan dai an kai al’amarin gaban alkali, kafin akai ga fara sauraron karar, sai aka rarrashi wacce aka yi wa rotsen har aka akai daidaiton cikin gida, da sharadin za’a dauki dawainiyar magungunata da suka shafi kanta da kuma yaron cikin nata, inda ana zuwa kotun sai ta ce ta yafe.

To amma daga baya tayi ikirarin an bar su da dawainiyar maganin, ta na ta faman wahala ga cuta taki ta kare, kullum ciwon kai babu barci, har takai an yi mata gwajin kwakwalwa, cikin da take dauke da shi kuma likita ya gwada ya ce yaron ya mutu, haka aka haife shi barai, sannan kuma ta zo ta na gwaba mata magana ta na cewar, wai ta yiwa banza harma ta na yi mata gwalo.

Kwanaki kadan da fauwar al’amarin, sai aka wayi gari ba’a ga wannan mata ba, inda matar ta bayyana cewar, garin ne ya yi mata zafi shi yasa tayi hijira.

Ya zuwa yanzu dai, da yake an gano ta, sai suka yanke shawarar a koma kotun ta shari’ar musulinci dake Goron Dutse, a bude karar a nema mata hakkinta.

Inda a zaman kotun na wannan lokaci kotun ta bukaci da aka kawo rubutacciyar sheda daga likita, ta kuma dage shari’ar zuwa 30 ga watan gobe.

A zantawar mu da mijin wadda ake zargin Idris Ahmad, bai yi musun cewa, matar tasa ta yi rotsen ko kaye akan yaron cikin ba, ya kuma tabbatar da cewa an yi sulhun sun kuma dauki nauyin maganin, amma duk wadanda ta ce taje ta biya a aljihunta, bada saninsu ta yi su ba, zancen fadar maganganu bayan sulhun kuwa, ya ce bashi da masaniya.

Alhaji Muhammad Bello Gadon Kaya shi ne shugaban kungiyar kare hakkin Dan adam da jin kai ta kasa wato Human Right Foundation of Nigeria, ya ce, suma sun ci karo da al’amarin a kotun kuma matar da mijinta sun shigar da korafi domin za su ci gaba da bin shari’ar.

 

 

 

 

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending