Connect with us

Labarai

Kano: Wata mata ta rotse kan facalar ta da tabarya

Published

on

Wata mata an yi zargin ta rotse kan facalar ta da tabarya, ta kuma kada ita a kan yaron cikin da ta dauke da shi, wadanda ke zaune a gida daya a unguwar Birget PRP a jihar Kano.

An yi zargin dai facalolin sabani ne ya gifta a tsakaninsu, inda matar kanin Khadija Isma’il, ta yi amfani da tabarya ta rotse kan matar wan mijin nata mai suna Jamila Shehu.

Bayan dai an kai al’amarin gaban alkali, kafin akai ga fara sauraron karar, sai aka rarrashi wacce aka yi wa rotsen har aka akai daidaiton cikin gida, da sharadin za’a dauki dawainiyar magungunata da suka shafi kanta da kuma yaron cikin nata, inda ana zuwa kotun sai ta ce ta yafe.

To amma daga baya tayi ikirarin an bar su da dawainiyar maganin, ta na ta faman wahala ga cuta taki ta kare, kullum ciwon kai babu barci, har takai an yi mata gwajin kwakwalwa, cikin da take dauke da shi kuma likita ya gwada ya ce yaron ya mutu, haka aka haife shi barai, sannan kuma ta zo ta na gwaba mata magana ta na cewar, wai ta yiwa banza harma ta na yi mata gwalo.

Kwanaki kadan da fauwar al’amarin, sai aka wayi gari ba’a ga wannan mata ba, inda matar ta bayyana cewar, garin ne ya yi mata zafi shi yasa tayi hijira.

Ya zuwa yanzu dai, da yake an gano ta, sai suka yanke shawarar a koma kotun ta shari’ar musulinci dake Goron Dutse, a bude karar a nema mata hakkinta.

Inda a zaman kotun na wannan lokaci kotun ta bukaci da aka kawo rubutacciyar sheda daga likita, ta kuma dage shari’ar zuwa 30 ga watan gobe.

A zantawar mu da mijin wadda ake zargin Idris Ahmad, bai yi musun cewa, matar tasa ta yi rotsen ko kaye akan yaron cikin ba, ya kuma tabbatar da cewa an yi sulhun sun kuma dauki nauyin maganin, amma duk wadanda ta ce taje ta biya a aljihunta, bada saninsu ta yi su ba, zancen fadar maganganu bayan sulhun kuwa, ya ce bashi da masaniya.

Alhaji Muhammad Bello Gadon Kaya shi ne shugaban kungiyar kare hakkin Dan adam da jin kai ta kasa wato Human Right Foundation of Nigeria, ya ce, suma sun ci karo da al’amarin a kotun kuma matar da mijinta sun shigar da korafi domin za su ci gaba da bin shari’ar.

 

 

 

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending