Connect with us

Labarai

‘Yan sanda sun cafke wani matashi dake yawo da almakashi

Published

on

Kotun Majestrate mai lamba 49 karkashin mai shari’a Hadiza Abdulrrahman, ta daure wasu matasa biyu, Sama’ila Jafar dan uwa Mai Dile, da kuma Ahmad Ali Bala.

Tunda fari dai ‘yan sandan Sheka ne suka gurfanar da matasan biyu inda aka tuhumi Sama’ila Jafar da laifin shan taba wiwi, domin yin maye, bayan kuma an karanta masa tuhumar da ake masa ne ya amsa, kotun kuma ta yiwa masa daurin watanni Hudu ko kuma ya biya tarar Naira Dubu Goma.

Haka zalika shima matashi Ahmad Ali Bala, an tuhumeshi ne da laifin samun sa da Almakashi, wanda bayan karanta masa kunshin tuhumar da ake yi masa shima ya amsa ba tare da wahalar da shari’a ba, a nan ne kotun ta yi masa daurin watanni Uku ko kuma ya biya tara ta naira Bubu Biyar.

Mai shari’a Hadiza Abdulrahman ta yi umarni ga jami’in gida  ajiya da gyaran hali, Babangida Sani da masu taimaka masa, Nasir Ado da Mubarak Sani Karkarna, da su wuce da su gidan ajiya da  gyaran hali.

Wakilin mu Hassan Mamuda Ya’u ya zanta da matasan, wadanda suka bayyana nadamar su a fili, wanda suka ce, matukar suka fita daga halin da suke ciki to za su yi kokari wajen ganin sun gujewa aikata laifi makamancin irin wanda suka yi har ma suka ja hankalin ‘yan uwansu matasa da su kaucewa aikata laifuffuka su zama mutane na gari.

 

 

 

 

 

 

 

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending