Connect with us

Labarai

Covid-19: Gwamnati ta kara kaimi wajen yaki da Corona -SEDSAC

Published

on

Kungiyar bunkasa ilimi da al’amuran jama’a da demokradiyya SEDSAC, ta al’umma na da rawar da za su taka wajen dakile yaduwar cutar Coronavirus a cikin zamantakewar al’umma wajen kulawa da yaduwar cutar ta hanyar rage cinkoso.

Cikin wata sanarwa mai kunshe da sa hannun babban daraktan kungiyar, Kwamrade Hamisu Kofar Na’isa, ya sanyawa hannu a ka kuma rabawa manema labarai, kungiyar ta ce kamata ya yi gwamnati ta sa dokar ta bace wajen hana zirga-zirgar ababan hawa a dukannin titinan jihohin kasar nan baki daya domin gudun yada cutar a cikin jihohin Nijeriya.

Sanarwa ta kuma ce gwamnati da ta kara tsaurara matakan kariya sosai domin yakar cutar Covid-19 domin kuwa cutar ta na da matukar hadari ga rayuwar al’ummar Nijeriya da ma duniya baki daya.

Sannan ta kuma bukaci al’umma da su ci gaba da bin umarnin jami’an lafiya da kuma shawarwarin su, gudun kamuwa da cutar ta Covid-19 tare da bin duk wasu hanyoyi da za a magance yafuwar cutar domin kare lafiya baki daya.

Haka zalika, ta kuma ce tabbas wannan cuta ta Covid-19 ta kawo tasgaro a fannin a fannin da sauran al’amura, domin haka kamata ya yi gwamnati ta dauki matakin gaggawa domin farfado da fannin ilimi da sauran al’amura baki daya.

Sannan ta kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta jiha da ta rage kudaden gudanar da manyan ayyukan gwamnati na wannan shekarar sakamakon farashin man fetur da ya yi kasa domin al’umma su amfana. Sakamakon cewa halin da a ke ciki na wajen tattalin arizki Nijeriya ta dogara da man fetur domin haka rage farashin man ba zai shafi tattalin arikin kasar nan ba.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending