Connect with us

Labarai

Covid-19: Gwamnati ta kara kaimi wajen yaki da Corona -SEDSAC

Published

on

Kungiyar bunkasa ilimi da al’amuran jama’a da demokradiyya SEDSAC, ta al’umma na da rawar da za su taka wajen dakile yaduwar cutar Coronavirus a cikin zamantakewar al’umma wajen kulawa da yaduwar cutar ta hanyar rage cinkoso.

Cikin wata sanarwa mai kunshe da sa hannun babban daraktan kungiyar, Kwamrade Hamisu Kofar Na’isa, ya sanyawa hannu a ka kuma rabawa manema labarai, kungiyar ta ce kamata ya yi gwamnati ta sa dokar ta bace wajen hana zirga-zirgar ababan hawa a dukannin titinan jihohin kasar nan baki daya domin gudun yada cutar a cikin jihohin Nijeriya.

Sanarwa ta kuma ce gwamnati da ta kara tsaurara matakan kariya sosai domin yakar cutar Covid-19 domin kuwa cutar ta na da matukar hadari ga rayuwar al’ummar Nijeriya da ma duniya baki daya.

Sannan ta kuma bukaci al’umma da su ci gaba da bin umarnin jami’an lafiya da kuma shawarwarin su, gudun kamuwa da cutar ta Covid-19 tare da bin duk wasu hanyoyi da za a magance yafuwar cutar domin kare lafiya baki daya.

Haka zalika, ta kuma ce tabbas wannan cuta ta Covid-19 ta kawo tasgaro a fannin a fannin da sauran al’amura, domin haka kamata ya yi gwamnati ta dauki matakin gaggawa domin farfado da fannin ilimi da sauran al’amura baki daya.

Sannan ta kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta jiha da ta rage kudaden gudanar da manyan ayyukan gwamnati na wannan shekarar sakamakon farashin man fetur da ya yi kasa domin al’umma su amfana. Sakamakon cewa halin da a ke ciki na wajen tattalin arizki Nijeriya ta dogara da man fetur domin haka rage farashin man ba zai shafi tattalin arikin kasar nan ba.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending