Connect with us

Labarai

Covid-19 Kungiyar daliban Tukuntawa TUYODA ta raba sinadarin wanke hannu a masallatai

Published

on

Kungiyar daliban unguwar Tukuntawa TUYODA, da sauran hadin gwiwar kungiyoyin yankin sun dauki gabaran gudanar da rabon sinadarin wanke hannaye a cikin masallatan fadin yankin baki daya.

Kungiyar wadda ta fara daukan wannan matakin a cikin makon nan domin dakile yaduwar annobar cutar Covid-19 a yankin unguwar Tukuntawa dake karamar hukumar  birni da kewaye.

Sinadaren wanke hannuun da kungiyar TUYODA ta hada

Yayin rabon sinadarin wanke hannayen, Sakataren kungiyar, Zahradeen Usaini Lizarazu, ya ce ”Muna bin layi-layi na fadin unguwar domin wayar da kan al’umma cewa wannan cuta ta Coronavirus gaskiya ce domin haka muka gayyato mai hada magunguna ya kuma koya mana yadda a ke hada sinadarin wanke hannu, kuma muna bi masallatai da loko-loko na unguwar mu na rabawa domin kare kai”.

A nasa jawabin shugaban kungiyar TUYODA, Fardeen Aliyu, cewa ya yi” Muna wayar da kan mu ne kafin a ce wata kungiya ta zo ta taimaka mana daga waje, saboda haka mu ka hadu muka kirawo sauran kungiyoyin mu na cikin unguwa domin wayar da kan al’umma wajen wanke hannayen mu kafin mu ci abinci ko taba wani abu, domin haka muka kirawo guda daga cikin me hada magunguna ya koya mana muka kuma hada mu ke bi cikin masallatai domin raba wannan abun wanke hannun, harma mu bi inda majalisa take mu raba masu”.

Shi kuwa mai hada maganin, Pharmacist Auwal Bala, inda ya ce” A matsayi nan a mazaunin unguwar Tukuntawa mun zauna mun dauki wannan matakin ne domin hada wannan sinadarin wanke hannu kuma wanda kungiyar lafiya ta duniya ta amince da shi, domin ita ta bayyana yadda zamu hada shi cikin sauki wanda mutum zai iya hadawa a gida kuma ga shi da kudi kadan muka hada saboda wancan ya yi tsada, saboda haka muke kira da masu hannu da shuni da sauran al’umma da su tashi tsaye wajen bada tallafi ga irin wadannan kungiyoyi domin su hada su kuma rabawa al’umma”.

Guda daga cikin wanda suka rabauta da sinadarin wanke hannun’ Rabi’u Abdullahi Abubakar Tukuntawa ya ce” Sai dai mu yi godiya ga wannan kungiya sakamakon dama mu bamu dashi sai dai mu wanke hannu da ruwan kumfa kuma tabbas mun ji dadin wannan batu na wayar da kai da TUYODA take yi a Tukuntawa” A cewar mazaunin unguwar.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending