Connect with us

Labarai

Za muyi maganin masu shigowa Kano ta barauniyar Hanya -Ganduje

Published

on

Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce, basu gamsu da yadda direbobi har yanzu suke shigowa jihar Kano ta barauniyar hanya da fasinjoji ba, a don haka zasu dauki matakan dakile ratsen da direbobin suke yi.

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne a zantawarsu da wakilinmu Abba Isah Muhammad, yayin wata ziyarar ganin yadda iyakar shigowa jihar Kano take gudana, a jiya Litinin.

Ya kuma ce, “Duk barauniyar hanyar da ake bi domin shigo da fasinjoji za mu toshe ta, inda direbobin kan ajiye fasinjojin a baya, sai su shigo su hadu a hanya su karaso da su cikin jihar Kano”. A cewar Ganduje.

Wani mai sana’ar Achaba mai suna Ibrahim mazaunin Kwanar Dangora ya ce, “Da safe na tashi naga an rufe gate, kuma samun kudi ada yafi, yanzu ba gashi kaga ana wucewa ba, daga nan kwanar Dangora, wasu na karbar dari biyar amma ni dari biyu nake karba”.

Haka zalika, wani mazaunin Tunkuna a karamar hukumar Kiru, Abdullahi Idris ya bayyana cewa, “Muna ganin halin da masu tafiya ke shiga, wani ma zai sauka bashi da abinda zai ci, kuma ga ma’aikata in an bi nan su tare. mu nan da ake tare wa ba zai taru ba, sai dai duk hayyoyin nan a rufe. Akwai hanya mai zuwa Faki, Jan Marmara dake jihar Kaduna zaka iya haurowa ka shigo Kano”.

Shima wani direban mota, Muhammadu Kabir, ya ce, “mu dai jihar Kano Alhamdulillahi. mu na kaucewa jami’an tsaro mu shigo jihar Kano, amma komai yana iya faruwa, tunda an ce cuta ce da take bin iska, bayan an sa dokar shigowa jihar Kano da fasinjoji, na shigo Kano yafi sau biyu”.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending