Connect with us

Labarai

Covid-19: Malaman islamiyya sun koka kan rufe makarantu

Published

on

Malaman makarantun islamiyya sun yi korafin ana nuna masu banbanci tsakaninsu da sauran malaman makarantu na gwamnati.

Shugaban kungiyar hadakan malaman makarantun isalamiyya da tsangayu a jihar Kano, Malam Kamalu Sa’idu Habibu ne ya bayyana haka a zantawarsu da gidan rediyon Dala.

Ya ce, “Tun bayan da aka dakatar da gudanar da makarantu mu ka shiga haliin tasku, kasancewar mun dogara ne da kudaden wata da na Laraba da muke karba daga iyayen yara, yanzu kuma tunda ba makarantun, to babu kudaden watan da Larabar”. Inji Malam Kamalu.

Kazalika, suma wasu daga cikin malaman makarantun islamiyar sun ce yanzu ta kai ga sun fara shiga wani mawuyacin hali, saboda rufe makarantun nasu.

Shugaban kungiyar kare hakkin dan adam ta Human Right Foundation of Nigeria, Alhaji Muhammad Bello Gadon Kaya ya ce, “Idan dan talaka ya sauke hakkinsa na yin biyayya ga dokar gwamnati, to shima fa yana da nasa hakkin a wajen gwamnati, kuma kwamitin nan na tattara tallafi wanda gwamnatin jiha ta kafa, to idan an tara tallafin kamata yayi a mayar da hankali wajen talakwa musamman ma wadanda suka shiga cikin rudani, sakamakon kullen na korona”. A cewar Alhaji Muhammadu

Babban kwamanda hukumar Hisba Sheikh Harun Ibn Sina daya ne daga cikin ‘yan kwamatin tattara tallafin, ya bayyana cewar, “Zamu mayar da hankali wajen talakawan, tunda dai al’umma sun amsa kiran, alat din shigar kudi kawai suke jira su ji ta kowacce fuska”. Inji Ibn Sina.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending