Connect with us

Labarai

Shekaru biyar da fitowar Kada daga gidan adana namun daji na Kano

Published

on

Yau kimanin shekaru biyar cif Kenan da wata katuwar Kada ta fito daga cikin gidan ajiye namun daji na Kano wato Zoo dake karamar hukumar birnin Kano.

Kadar dai ta fito ne ta hanyar magudanan ruwa ta kuma shigo ciki unguwar da take da makwabtaka da gidan wato unguwar Tukuntawa, a nan ne jama’ar gari su ka kula da giftawar kadar a lokacin da kafa ta dauke.

Sai dai a wancan lokacin a shekarar 2015 katuwar Kadar ta dauki hankalin mutanen yankin wanda su ka rinka dauki ba dadi da ita a lokacin da ta fito shan iska, su ka kuma yi gaggawar sanar da mahukuntan gidan ajiye namun dajin tun a wancan lokacin, sai dai kuma kama Kadar ya yi wuya sakamakon wata kwata da ta shiga wadda ba a iya shiga cikin ta sakamakon ta bulle ta kan titi.

Tun a lokacin ne wasu matasa tare da mafarauta a yankin na Tukuntawa su ka yi kokarin kama kadar har su ka tare a lokacin amma hakan su bai cimma ruwa ba, sai dai a lokacin a ka samu sa’a kadar ta fito cikin tsakiyar dare wasu matasa a yankin su ka yi kokarin kama kadar tare da mika ta cikin gidan ta, kamar yadda ku ke ganin ta a hoto.

Lokacin da matasan su ka kama Kada a unguwar Tukuntawa

Labarai

NAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa Saudiyya

Published

on

Yanzu haka hukumar Aikin Hajji ta ƙasa NAHCON, ta 15 ga watan nan na Mayun 2024, a matsayin ranar da za’a fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana, zuwa ƙasa mai tsarki.

Bayanin hakan ya fito ne ta bakin shugaban hukumar ta NAHCON, Jalal Ahmad Arabi, a wajen taron masu ruwa da tsaki kan aikin Hajji da Umrah, da ya gudana yau Alhamis birnin tarayya Abuja.

“Maniyyata kimanin 65,500 ne za su sauke Farali daga ƙasar nan a ƙasa mai tsarki; za su shafe aƙalla kwanaki huɗu domin yin ziyara a Madina kafin fara aikin Hajji, “in ji Arabi”.

Daga bisani shugaban hukumar aikin hajjin Jalal Ahmad Arabi, ya kuma bayyana cewa za ayi jigilar maniyyata aikin hajjin ne daga cibiyoyi 10 a faɗi ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

Olubunmi, ya kuma sake nanata buƙatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkanib matakai daban-daban.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur ta haifar mana da koma baya a sana’ar mu – Mai Motar Haya

Published

on

Wani mai sana’ar tuƙin motar Haya, da kuma lodin fasinjoji mai suna Kabiru Muhammad, mazaunin ƙaramar hukumar Munjibir, ya ce ƙarancin motocin Haya da ake samu a yanzu, yana da alaƙa da wahalar man Fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya.

A zantawar mutumin da wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il, ta cikin shirin rahotanni daga ƴan Zazu na yau Talata, ya ce a baya har motoci hamsin suke yiwa lodin fasinjoji su tashi, amma a yanzu Mota ɗaya suke iya cikawa sakamakon ƙarancin Fetur da ake fama da shi.

Ya kuma ce ƙaranci tare da tsadar man fetur ɗin da ake fama da shi, sun haddasa musu koma baya a sana’ar su, baya ga batun kuma matsalar da suke fuskanta da fasinjoji wajen biyan kuɗin Mota.

Wakiliyarmu da ta bibiyi shirin na ƴan Zazu Ummi Bala Ahmad ta rawaito cewa, matuƙin motar Kabiru Muhammad, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jahohi, da su yi abinda ya kamata dan ganin farashin man Fetur ɗin ya sauka, domin al’umma su samun sauƙi.

Continue Reading

Trending