Connect with us

Labarai

Marayu 324 su ka samu kayan sallah a unguwar Tukuntawa

Published

on

Cibiyar tallafawa marayu na Masjid Kuba dake unguwar Tukuntawa a karamar hukumar birni a jihar Kano, ta rabawa marayu maza da mata kimanin 324 kayan sallah dake fadin yankin.

Rabon kayan sallah ga marayun ya gudana a harabar masallacin Juma’a na unguwar Tukuntawa.

Shugaban kungiyar, Adam Musa Dan Azumi ke jawabi a yayin taron.

Shugaban kungiyar, Adam Musa Dan Azumi, ya ce” Wannan dai shi ne kashi na shida da mu ka yi rabon kayan wato yau shekaru shida kenan mu na yi, mun raba kayan sallah na marayu su mutum 324 a tsakanin maza da mata wanda mu ka gayyaci yaran da ba su wuce hamsin ba, saboda dokar hana taruwa da yawa, wannan shi ma mu na samun taimako ne daga daliban makarantar Gharu Hira bangaran matan aure da kuma wasu na waje kamar su Engr. Shehu Ibrahim Khalil Baban Raga da wasu da yawa da su ka bamu gudunmawa musammamma shi Engr ya dau nauyin yara mutum dari da saba’in mata dari da goma sha biyar sai ragowar maza, kuma taron ya sami hallartar dagacin unguwar Gandu da mai unguwar Tukuntawa da mai unguwar Kwandilar Gandu da shi kansa Engr. Ibrahim Khalil da sauran Malan makaranta karkashin shugabancin makarantar Mal Nura Umar Abdulaziz”. A cewar sa.

Cibiyar tallafawa marayu ta Gharu Hira ta kum Ja hankalin mawadata da su fito su taimaka a irin wannan aikin sakamakon mawuyacin halin da marayu ke sha a rayuwar su.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending