Connect with us

Labarai

Covid-19: Yadda gwajin Corona ke tafiya a Kano

Published

on

Tun bayan bullar cutar Covid-19 a Kano a kan samu wasu ranaku da ba a samu karin wadanda a ka gano su na dauke da cutar ba.

Ko a ranar Asabar 16 ga watan Mayun da mu ke ciki, ba a samu ko mutum guda dake dauke da cutar ba a Kano, haka abun yake a ranar Talata 19 ga watan Mayun.

Farfesa Isah Sadiq Abubakar shi ne shugaban sashen gwaje-gwajen cututtuka masu yaduwa na jami’ar Bayero dake jihar Kano, domin jin shin ko hakan ya na nufin an tasamma kassara cutar a Kano?

Ya ce “A’a ba za mu yi saurin daukar hakan ba, domin yin hakan zai zama wani ganganci, domin idan a ka dauka anyi nasarar dakile wannan cuta tun yanzu to kaga mutane za a yi sake, daga mu masu yakar abun zuwa mutanen gari. Ganin cewa ba a samu case ba na kwana daya abu ne da zai faranta mana rai, amma kuma kwana daya ba komai bane a wannan yaki, har sai in an samu hakan ya dore zuwa wani lokaci, mun ga cewa abun ba a samun bullar cutar shi ne  za mu yi wannan murna cewa an fara samun nasara”.

Ko a kwai mutanen da ku ka yi wa gwaji a ranar Asabar din kuma a ka samu basa dauke da cutar, domin haka ya zama “0 Case” ko yaya?

“To akwai dakunan gwaji guda 3 a Kano, amma na san a dakin da nake shugabanci na jami’ar Bayero ba muyi gwajin Kano ko guda daya ba a wannan rana, ban san sauran dakunan gwajin ba. Mu a wurin mu ranar mun yi aikin da a ka aiko mana daga jihohin Katsina da Jigawa, amma Jigawa sun aiko guda 600, Katsina kuma sun aiko da guda 200 to sai ranar Lahadi mu ka yi aikin na Kano”.

A kididdigar da ku ke fitarwa ta adadin wadanda su ka kamu ko su ka warke a kullum, ko akwai yi wuwar ku rika fitarwa dauke da adadin wadanda ku ka yi wa gwaji a kullum, a cikin su ga wadanda su ka kamu domin jama’a su rinka rarrabewa?

 

“Eh, ya kamata dai kam, wannan tsari ne me kyau kuma kwamiti na jiha zai yi hakan nan bada jimawa ba. Inji Farfesa Isah.

Tattaunawar mu da Farfesa Isah Sadiq Abubakar shugaban sashen gwaje-gwajen cututtuka masu yaduwa na jami’ar Bayero dake jihar Kano.

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Labarai

Iyaye ku dai ma marawa ƴaƴan ku baya akan abinda suke yi da ya saɓawa doka – Mai unguwar Ja’en Jigawa

Published

on

Mai unguwar Ja’en Jigawa da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano Sani Muhammad, ya ce bai kamata a rinƙa samun wasu iyaye da ɗabi’ar nan ta marawa ƴaƴan su baya akan abinda yaran suke aikatawa na saɓawa Doka, domin gujewa abinda ka je ya dawo.

Mai unguwar ya bayyana hakan ne yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a lokacin da yake tsokaci kan yadda ake samun wasu daga cikin iyayen yankin sa na marawa ƴaƴan su baya kan abinda suke yi na ba dai dai ba, lamarin da yake ƙara ƙara kangarar da tarbiyyar ƴaƴan tare da tayar da hankalin al’umma.

Mai unguwa Sani Muhammad, ya kuma ce matuƙar yaran ba za su zauna lafiya a cikin unguwa da al’umma ba, to kuwa za su rinƙa ɗaukar matakin miƙa yaran hannun jami’an tsaro mafi kusa, domin ɗaukar matakin da ya dace a kan su, wajen ganin sun sauke nauyin da aka ɗora musu.

Sani Muhammad, ya ƙara da cewa ko a baya bayan nan wasu matasa sai da suka yi yunƙurin yin abinda bai kamata ba, lamarin da yasa aka ɗauki mataki a kansu amma aka samu wasu daga cikin iyaye suka marawa yaran nasu baya, wanda hakan kan haifar da barazanar tsaro.

Continue Reading

Labarai

Matasa ku ƙara dagewa da neman Ilmin addini da na zamani – Dr. Abdallah Gadan Kaya

Published

on

Fitaccen malamin addinin Musluncin nan Dakta Abdallah Usman Umar, ya shawarci matasa da su ƙara mayar da hankali wajen neman ilmin addinin da na zamani, domin zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Dakta Abdallah Gadan Ƙaya, ya bayyana hakan ne ta cikin Tafsirin Al-ƙur’ani mai girma, da yake gabatarwa cikin wannan watan azumin Ramadana a jihar Gombe.

A cewar sa, “Akwai buƙatar matasa ku yi riƙo da ƙananan sana’o’in dogaro da kai, da za ku rinƙa biyawa kan ku kuɗin makaranta wajen neman ilimi domin kaucewa zama a cikin jahilci, “in ji shi”.

Dakta Abdallah, ya kuma yi kira ga shugabanni da su dukkan abinda ya dace wajen inganta makarantu a sassan ƙasar nan, domin ganin ɗalibai sun samu ingantaccen Ilmi.

Continue Reading

Trending