Connect with us

Labarai

Covid-19: Yadda gwajin Corona ke tafiya a Kano

Published

on

Tun bayan bullar cutar Covid-19 a Kano a kan samu wasu ranaku da ba a samu karin wadanda a ka gano su na dauke da cutar ba.

Ko a ranar Asabar 16 ga watan Mayun da mu ke ciki, ba a samu ko mutum guda dake dauke da cutar ba a Kano, haka abun yake a ranar Talata 19 ga watan Mayun.

Farfesa Isah Sadiq Abubakar shi ne shugaban sashen gwaje-gwajen cututtuka masu yaduwa na jami’ar Bayero dake jihar Kano, domin jin shin ko hakan ya na nufin an tasamma kassara cutar a Kano?

Ya ce “A’a ba za mu yi saurin daukar hakan ba, domin yin hakan zai zama wani ganganci, domin idan a ka dauka anyi nasarar dakile wannan cuta tun yanzu to kaga mutane za a yi sake, daga mu masu yakar abun zuwa mutanen gari. Ganin cewa ba a samu case ba na kwana daya abu ne da zai faranta mana rai, amma kuma kwana daya ba komai bane a wannan yaki, har sai in an samu hakan ya dore zuwa wani lokaci, mun ga cewa abun ba a samun bullar cutar shi ne  za mu yi wannan murna cewa an fara samun nasara”.

Ko a kwai mutanen da ku ka yi wa gwaji a ranar Asabar din kuma a ka samu basa dauke da cutar, domin haka ya zama “0 Case” ko yaya?

“To akwai dakunan gwaji guda 3 a Kano, amma na san a dakin da nake shugabanci na jami’ar Bayero ba muyi gwajin Kano ko guda daya ba a wannan rana, ban san sauran dakunan gwajin ba. Mu a wurin mu ranar mun yi aikin da a ka aiko mana daga jihohin Katsina da Jigawa, amma Jigawa sun aiko guda 600, Katsina kuma sun aiko da guda 200 to sai ranar Lahadi mu ka yi aikin na Kano”.

A kididdigar da ku ke fitarwa ta adadin wadanda su ka kamu ko su ka warke a kullum, ko akwai yi wuwar ku rika fitarwa dauke da adadin wadanda ku ka yi wa gwaji a kullum, a cikin su ga wadanda su ka kamu domin jama’a su rinka rarrabewa?

 

“Eh, ya kamata dai kam, wannan tsari ne me kyau kuma kwamiti na jiha zai yi hakan nan bada jimawa ba. Inji Farfesa Isah.

Tattaunawar mu da Farfesa Isah Sadiq Abubakar shugaban sashen gwaje-gwajen cututtuka masu yaduwa na jami’ar Bayero dake jihar Kano.

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Trending