Connect with us

Labarai

KAROTA ba ta da hurumin yi wa mutane tara a kan kullen Corona -Baba Jibo

Published

on

Wasu mutane a birnin Kano sun yi kukan cewar Jami’an hukumar KAROTA su na kama su a cikin masallacin Idi a yi musu tarar kudade har Naira dubu biyar.

Masu korafin dai sun bayyana cewar sakamakon dokar kulle Jami’an jami’an na yi mu su tara a cikin masallacin idi. A ida a ke yankewa masu babur hukuncin biyan tarar dubu uku yayin da mu su babur mai kafa uku a ke yanke masu hukuncin biyan tarar dubu biyar.

Wakilin mu Yusuf Nadabo Ismail ya kai ziyara masallacin Idin, ya kuma iske tarin masu babura wadanda su ke jiran a yanke musu hukunci a lokacin.

Harma wakilin na mu ya zanta da wasu daga cikin mutanen wadanda su ka bayyana yadda a ke yi mu su tara, Usaini Abdullahi mazaunin unguwar Gidan Zoo wanda ya ce” Na kawo wani mara lafiya zuwa asibitin Murtala kawai sai na ji kawai an kama ni a ka kai ni cikin filin Idi tare da cin tara ta”.

Shi kuwa wani matashi mai suna Magaji Idris cewa ya yi Na je ‘yan Lemon a kawo lemo zuwa cikin Fagge kawai sai wani jami’in KAROTA ya kama ni ya kai ni cikin masallacin Idi a ka kuma cini tarar dubu biyar.

Sai dai kakakin kotunan jihar Kano, Baba jibo ya ce”KAROTA ba su da hurumin yin tara a harkar kullen covid 19, domin kuwa wannan ba hurumin ta ba ne”.

Mun kuma tuntubi mai magana da yawun hukumar KAROTA Nabulisi Abubakar Kofar Na’isa wanda ya bayyana cewar” Wanda ya tabbata ya yi laifi kotu c eke da ikon ta ci tarar mutum kawai dai idan jami’an sun kama mutum za su kai su wajen kotun tafi da gidan ka a yanke mu su hukunci”.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending