Connect with us

Labarai

Ba za mu yarda a yi taron Idin Kwakwa ba a wannan lokaci -‘Yan Sanda

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta yi wata ganawa ta musamman da ‘yan kwamitin masallacin Abdullahi Suka dake garin Zawaciki dake yankin karamar hukumar Kumbotso da kuma Dagacin yankin bisa yadda a ke gudanar da al’adar taron jama’a a masallacin wanda a ke wa lakabi da idin Kwakwa bayan sallar Idi wanda ‘yan mata da samari ke taruwa.

Baturen ‘yan sandan yankin Muhammad Talba ne ya jagoranci zaman ganawar a yunkurin hukumar na dakatar da cunkuso domin dakile yaduwar cutar Corona a fadin jihar da ma kasa baki daya.

A nasa bangaren limamin masallacin Abdullahi Suka, Alhaji Muhammad Sabi’u Zawaciki kiran mutane ya yi da su kiyaye bin dokokin da a ka sanya wajen gudanar da sallar Idin.

Da yake jawabi yayin ganawar Malam Alhassan Ibrahim wanda shi ne shugaban kwamitin masallacin ya bayyana cewar” Za mu ja hankalin mutane yayin gudanar da huduba ba saye babu siyarwa kowa ya na idar da sallar Idin kowa ya koma gida domin kiyaye dokar da a ke ciki ta zaman gida”.

Shi ma Dagacin yankin, Alhaji Abdulkadir Mu’azu Zawaciki ya kara baiwa al’umma hakuri cewa” Ku daure ku bi dokokin, domin komai sai da lafiya a ke yin sa kuma addinin ma haka ya koyar”.

Wakilin mu Sayyadi Haruna Kutama ya ruwaito cewar ma su ruwa da tsaki a kan lamuran masallacin sun bayyana cewa za su yi iya yin su wajen ganin an bi dokokin yadda ya kamata.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending