Connect with us

Labarai

Manoman Masara a Kano sun ci gajiyar rance daga CBN

Published

on

Shugaban kungiyar manoma Masara da sarrafa ta da kuma kasuwancinta ta kasa reshen jihar Kano (MAGPAMAN), Yusuf Ado Kibiya ya ce tsarin da bankin CBN ya bijiro da shi na tallafawa ‘ya’yan kungiyar abun nasara ne babba ga manonam jihar da ma manoma baki daya.

A yayin kaddamar da rabon bada tallafi ciki harda takin zamani da masara da kuma magungunan kwari da a ka kaddamar a karo na farko a dakin taro na cibiyar addinin musulunci dake karamar hukumar Tarauni.

Ya ce” Wannan tallafin an yi shi ne domin manoma saboda shi ne tushen arziki, kuma wanna tsari shi ne na farko da a ka fara, domin akwai noman rani da na damuna, kuma ‘ya’yan kungiyar su yi kokari wajen yin amfani da damar da su ka samu”.

Kakakin kungiyar Sani Haruna Limawa cewa ya yi” Manoma su yi kokari su aiki tukuru domin kuwa su tabbata sun dawo wa da gwamnati hakin ta domin ta samu damar baiwa wasu al’umma”.

Su kuwa wasu daga cikin wadan da su ka samu tallafin sun ce za su yi iya kokarin su wajen ganin sun yi amfani da damar da su ka samu.

A kalla babban bankin Nijeriya CBN ya tantance Manoma dubu biyar da dari bakwai da sittin da hudu a kungiyar wanda tuni a ka fara baiwa mutane dubu biyu da dari bakwai daga cikin su.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending