Connect with us

Labarai

An kama dan sandan da ya takurawa wata budurwa a Kano

Published

on

Wata mata da ke unguwar Hotoro bayan Depot ta kai korafin wani jami’in Dan sanda a shelkwatar rundunar ‘yan sandan jihar Kano bisa zargin takurawa rayuwar ta da kuma cin zarafin ta da ya ke yi.

Matar ta kai korafin jami’in Dan sandan ne mai aiki a unguwar ta Hotoro ranar Alhamis domin a yi mata iyaka da shi.

Ta ce, “Akwai wani Dan sanda da a ke cewa Dan masani, to ya takurawa rayuwa ta, bayan an kai kara ta ya kamani a kan laifin da ba a bincike ni ba, ba’ a yi min komai ba, bayan na dawo gida kullum ya na bibiya ta ya na takurawa rayuwa ta. Ya taba zuwa ya same ni ba da kwakwkwaran sutura a jiki na ba, ya ce lallai sai na hau mota mun tafi, mutanen unguwa su ka fito su na ba shi hakuri ya ce, zai hada da su. Ni ba matar aure ba ce. Yanzu abubuwan sun yawa sai na kira dakin korafi na ‘yan sanda, kuma na zo na ga adalci karara, na gode wa Allah an taimaka min, kuma an kamo shi. Ba wani abu da yake kawo shi kawai in ya zo ya ce, in hau mota, ko kuma akwai kanne na mata guda biyu ya ce, suma lalle sai ya tafi da su”.

Ta kara da cewa, “Ya kamani ina jinin al’ada, na yi na yi ya barni in gyara jiki na, karshe ma’aikatan su ka ce ya barni in gyara jiki na ya ce a’a, har ya kasance su na kora ta saboda ina bata mu su wuri da jini, shi ne dalilin ya sa na kawo karar shi, ya na nan an kamo shi. Ni abun da na gani an taimake ni, kuma an gurfanar da shi a gaban manyan sa, kuma an yi adalci daidai gwargwado. Matakin da na ke so a dauka a raba ni da shi babu ni babu shi. Iya sanina abun da ya taba hada ni da shi ya taba cewa in bashi hadin kai naki”. A cewar matar.

A nasa bangaren Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce, “Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, ya sa an kamo wannan Dan sanda kuma ya bada umarnin a yi binciken kwakwaf, duk wanda ya ke da gaskiya a ciki, za ta bayyana kuma za a yi adalci. Kai tsaye kowanne lokaci mu na bada lambar ofishin mu, ko kuma a zo kai tsaye, ko a je ofishin mu da ke kusa a sanar da D.P.O, shi kuma ya turo mutane zuwa ofishin na mu”. Inji DSP Kiyawa.

Wakilin mu Abba Isah Muhammad ya rawaito cewa, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya kuma ja hankalin sauran jami’an ‘yan sanda da su yi aiki da gaskiya da rikon amana kamar yadda doka ta tanadar.

 

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Labarai

Iyaye ku dai ma marawa ƴaƴan ku baya akan abinda suke yi da ya saɓawa doka – Mai unguwar Ja’en Jigawa

Published

on

Mai unguwar Ja’en Jigawa da ke ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano Sani Muhammad, ya ce bai kamata a rinƙa samun wasu iyaye da ɗabi’ar nan ta marawa ƴaƴan su baya akan abinda yaran suke aikatawa na saɓawa Doka, domin gujewa abinda ka je ya dawo.

Mai unguwar ya bayyana hakan ne yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a lokacin da yake tsokaci kan yadda ake samun wasu daga cikin iyayen yankin sa na marawa ƴaƴan su baya kan abinda suke yi na ba dai dai ba, lamarin da yake ƙara ƙara kangarar da tarbiyyar ƴaƴan tare da tayar da hankalin al’umma.

Mai unguwa Sani Muhammad, ya kuma ce matuƙar yaran ba za su zauna lafiya a cikin unguwa da al’umma ba, to kuwa za su rinƙa ɗaukar matakin miƙa yaran hannun jami’an tsaro mafi kusa, domin ɗaukar matakin da ya dace a kan su, wajen ganin sun sauke nauyin da aka ɗora musu.

Sani Muhammad, ya ƙara da cewa ko a baya bayan nan wasu matasa sai da suka yi yunƙurin yin abinda bai kamata ba, lamarin da yasa aka ɗauki mataki a kansu amma aka samu wasu daga cikin iyaye suka marawa yaran nasu baya, wanda hakan kan haifar da barazanar tsaro.

Continue Reading

Labarai

Matasa ku ƙara dagewa da neman Ilmin addini da na zamani – Dr. Abdallah Gadan Kaya

Published

on

Fitaccen malamin addinin Musluncin nan Dakta Abdallah Usman Umar, ya shawarci matasa da su ƙara mayar da hankali wajen neman ilmin addinin da na zamani, domin zama ababen koyi a tsakanin al’umma.

Dakta Abdallah Gadan Ƙaya, ya bayyana hakan ne ta cikin Tafsirin Al-ƙur’ani mai girma, da yake gabatarwa cikin wannan watan azumin Ramadana a jihar Gombe.

A cewar sa, “Akwai buƙatar matasa ku yi riƙo da ƙananan sana’o’in dogaro da kai, da za ku rinƙa biyawa kan ku kuɗin makaranta wajen neman ilimi domin kaucewa zama a cikin jahilci, “in ji shi”.

Dakta Abdallah, ya kuma yi kira ga shugabanni da su dukkan abinda ya dace wajen inganta makarantu a sassan ƙasar nan, domin ganin ɗalibai sun samu ingantaccen Ilmi.

Continue Reading

Trending