Connect with us

Labarai

An kama dan sandan da ya takurawa wata budurwa a Kano

Published

on

Wata mata da ke unguwar Hotoro bayan Depot ta kai korafin wani jami’in Dan sanda a shelkwatar rundunar ‘yan sandan jihar Kano bisa zargin takurawa rayuwar ta da kuma cin zarafin ta da ya ke yi.

Matar ta kai korafin jami’in Dan sandan ne mai aiki a unguwar ta Hotoro ranar Alhamis domin a yi mata iyaka da shi.

Ta ce, “Akwai wani Dan sanda da a ke cewa Dan masani, to ya takurawa rayuwa ta, bayan an kai kara ta ya kamani a kan laifin da ba a bincike ni ba, ba’ a yi min komai ba, bayan na dawo gida kullum ya na bibiya ta ya na takurawa rayuwa ta. Ya taba zuwa ya same ni ba da kwakwkwaran sutura a jiki na ba, ya ce lallai sai na hau mota mun tafi, mutanen unguwa su ka fito su na ba shi hakuri ya ce, zai hada da su. Ni ba matar aure ba ce. Yanzu abubuwan sun yawa sai na kira dakin korafi na ‘yan sanda, kuma na zo na ga adalci karara, na gode wa Allah an taimaka min, kuma an kamo shi. Ba wani abu da yake kawo shi kawai in ya zo ya ce, in hau mota, ko kuma akwai kanne na mata guda biyu ya ce, suma lalle sai ya tafi da su”.

Ta kara da cewa, “Ya kamani ina jinin al’ada, na yi na yi ya barni in gyara jiki na, karshe ma’aikatan su ka ce ya barni in gyara jiki na ya ce a’a, har ya kasance su na kora ta saboda ina bata mu su wuri da jini, shi ne dalilin ya sa na kawo karar shi, ya na nan an kamo shi. Ni abun da na gani an taimake ni, kuma an gurfanar da shi a gaban manyan sa, kuma an yi adalci daidai gwargwado. Matakin da na ke so a dauka a raba ni da shi babu ni babu shi. Iya sanina abun da ya taba hada ni da shi ya taba cewa in bashi hadin kai naki”. A cewar matar.

A nasa bangaren Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce, “Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, ya sa an kamo wannan Dan sanda kuma ya bada umarnin a yi binciken kwakwaf, duk wanda ya ke da gaskiya a ciki, za ta bayyana kuma za a yi adalci. Kai tsaye kowanne lokaci mu na bada lambar ofishin mu, ko kuma a zo kai tsaye, ko a je ofishin mu da ke kusa a sanar da D.P.O, shi kuma ya turo mutane zuwa ofishin na mu”. Inji DSP Kiyawa.

Wakilin mu Abba Isah Muhammad ya rawaito cewa, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya kuma ja hankalin sauran jami’an ‘yan sanda da su yi aiki da gaskiya da rikon amana kamar yadda doka ta tanadar.

 

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending