Connect with us

Labarai

WATA TANKAR DAKON MAI TA KAMA DA WUTA A GARIN LEGOS.

Published

on

Wata tankin dakon mai ta kama da wuta a Legas da ke Najeriya, inda jami’ai suka ce gobarar ta kashe akalla mutum tara.

Sama da motoci 50 ne wadanda suka hada da bas-bas, suka kama da wuta a lokacin da motar makare da mai ta kufce, sannan man da take dauke da shi ya malale a kan hanya.

An ce motar ta fadi ne sanadiyyar katsewar burki.

Gobarar motocin dakon mai abu ne da aka saba gani a Najeriya, wadda ita ce kasar da ta fi kowacce fitar da mai daga Afirka zuwa kasuwannin duniya.

Ana safarar irin wannan mai ne ta hanyoyin mota a kasar, wadanda ba su cika samun kulawa ba.

Gobarar ta ranar Alhamis, ta faru ne da misalin karfe biyar da rabi na yamma, a kan babbar hanyar da ta tashi daga Ibadan zuwa cikin birnin na Legas.

Gobarar ta faru ne a lokacin da al’umma da dama ke zirga-zirga

Wani jami’in hukumar kiyaye afkuwar hadurra ta kasar FRSC, ya shaida wa BBC cewa motar ta kwace ne a lokaci da ta tun kari wata gada, sannan ta kife a gefen gadar.

A wannan lokaci ne mai ya rinka kwarara daga cikiin motar, abin da ya haddasa gobara, wadda ta bazu zuwa saurarn motoci.

Hotunan wurin da abin ya faru sun nuna yadda bakin hayaki ya turnuke sararin samaniyar wajen, da kuma fankon motocin da suka kone.

Hanyar Ibadan zuwa Legas na daga cikin manyan hanyoyin shiga birnin Legas

Shugaban kasar Muhammadui Buhari, ya ce ya yi bakin ciki game da asarar rayukan da aka yi.

A cikin wata sanarwa, shugaban ya ce “Wannan na daya daga cikin hadurra mafi muni da aka samu a baya-bayan nan”.

Wani mai magana da yawun gwamnati Kehinde Bamigbetan, ya ce “Lokaci ya yi da za a tabbatar da cewa mutane masu hankali ne sosai kawai suke tuka irin wadannan motoci na dakon mai.”

 

Labarai

Shugabanni ku fito da sabbin dabaru domin kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta tsadar rayuwa a ƙasa – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Universal Declaration of Human Rights dake jihar Kano, ta ce akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya dace dan ganin an kawo karshen matsalar tsaro, da kuma ta harkar tsaro dake ci gaba da addabar mutane a sassa ƙasar nan.

Daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Sani Galadanci, ne ya bayyana hakan yayin zantwarsa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Laraba, ya ce yadda ake ƙara samun ƴan ta’adda suna sace mutane tare da kashe su a sassan ƙasar nan, da kuma halin matsin rayuwar da ake fuskanta akwai buƙatar shugabanni suyi abinda ya kamata dan ganin an kawo ƙarshen matsalolin.

“Yawaitar kai hare-haren da ake samu daga ɓangaren ƴan bindiga a cikin al’ummar gari akan kashe su tare da sace su matuƙar ana son a kawo karshen matsalar, sai an ƙara himma wajen samar da makamai ga jami’an tsaro tare da samar da sabbin dabaru domin kawar da matsalar, “in ji Galadanci”.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki kaɗan da sako ɗalibai aƙalla su sama da 285, na makarantar Kuriga dake ƙaramar hukumar Chikun ta jihar Kaduna, da ƴan bindiga suka sace su a baya, baya ga wasu ɗaliban da aka sace a wata makarantar Tsangaya a jihar ta Kaduna, wanda ko a jihar Borno ma aka jiyo yadda aka sace ƴan gudun hijira da dama a baya-bayan nan, inda matsalolin tsaron ke ƙara yin gaba a sassan ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Kano ya kafa kwamitin duba yadda ake rabon tallafin abincin Azumi

Published

on

Gwamnatin Kano ta kafa kwamitin duba yadda ake ciyarwar azumin watan Ramadan, a kananan hokumomin cikin birnin jihar 8, domin sa ido da duba yadda ake gudanar da aikin dafawa da rabawa al’umma abincin.

Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya kafa kwamitin ne ƙarƙashin kulawar mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da wasu ƴan kwamitin.

Hakan na zuwa ne dai bayan da gwamna Abba Kabir, ya ziyarci wasu daga cikin wuraren da ake dafa abincin, inda ya nuna rashin jin daɗin sa kan yadda ya ga aikin ke gudana a karamar hukumar kumbotso.

Bayanin hakan ya fito ne ta cikin wata sanarwar da babban mai taimakawa gwamnan Kano, na musamman akan gidajen rediyo Bashir Aminu Fanshekara, ya aikowa manema labarai, ya ce an bayyana Alhaji Danyaro Yakasai, a matsayin wanda zai jagoranci kwamitin mai mambobi 7.

Fanshekara ya ce kwamitin ya fara zagayawa wasu daga cikin mazaɓu dake karamar hukumar kumbotso, domin duba yadda ake dafawa da kuma raba abincin tallafin ga al’umma, inda suka suka fara da mazaɓar Na’ibawa a ranar Asabar 23 ga watan Maris ɗin shekarar 2024.

Continue Reading

Ilimi

Kaduna:- Daliban Kuriga sun sha ki iskar ‘yanci

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da rahoton cewa an sako duka ɗaliban makarantar Kuriga da ƴanbindiga suka sace.

 

An sace ɗaliban firamare da na sakandare su kusan 287 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna fiye da makonni biyu da suka wuce.

 

Sanarwar da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya fitar ta ce an sako duka ɗaliban kuma suna cikin koshin lafiya.

 

Sanarwar ba tayi karin bayani ba game da irin matakan da aka bi wajen sako ɗaliban, sai dai gwamna Uba Sani ya nuna godiya ga shugaba Tinubu da mai bashi shawara kan tsaro da kuma sojojin Najeriya saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an sako ɗaliban.

 

“Ba dare babu rana ina tattaunawa da Malam Nuhu Ribadu domin lalubo hanyoyin da za a bi wajen kubutar da daliban, kafin mu samu nasara,” in ji Uba Sani.

 

Galibinsu ɗaliban da aka sace ƴan shekaru biyar ne zuwa 18.

Continue Reading

Trending