Connect with us

Wasanni

Manchester United ta sha da kyar

Published

on

Manchester United ta sami tikitin zuwa gasar cin kofin zakarun kungiyoyin nahiyar turai bayan da ta lallasa Leicester City da ci biyu da nema a filin wasa na King Power Stadium.

Ita kuwa Bournemouth ta fada ajin rukuni na biyu bayan tsawon shekara biyar da ta yi a gasar Firimiya, a yayin da Watford da Norwich City su ka nitse daga gasar.

Sakamakon wasan karshe na kakar 2019-2020.

  • Arsenal 3 Watford 2
  • Burnley 1 Brighton & Hove Albion 2
  • Chelsea 2 Wolverhampton Wanderers 0
  • Crystal Palace 1 Tottenham Hotspur 1
  • Everton 1 AFC Bournemouth 3
  • Leicester City 0 Manchester United 2
  • Manchester City 5 Norwich City 0
  • Newcastle United 1 Liverpool 3
  • Southampton 3 Sheffield United 1
  • West Ham United 1 Aston Villa 1
  • #             Sunayen Kungiyoyi                          P             GD          Pts
  • 1              Liverpool                                         38               52           99
  • 2              Manchester City                            38             67           81
  • 3              Manchester United                       38             30           66
  • 4              Chelsea                                             38            15           66
  • 5              Leicester City                                  38           26           62
  • 6              Tottenham Hotspur                       38           14           59
  • 7              Wolverhampton Wanderers         38           11           59
  • 8              Arsenal                                              38           8              56
  • 9              Sheffield United                               38           0              54
  • 10           Burnley                                                38           -7            54
  • 11           Southampton                                      38           -9            52
  • 12           Everton                                                38           -12          49
  • 13           Newcastle United                               38            20          44
  • 14           Crystal Palace                                      38            19          43
  • 15           Brighton & Hove Albion                    38             -15          41
  • 16           West Ham United                               38            -13          39
  • 17           Aston Villa                                            38            -26          35
  • 18           AFC Bournemouth                             38            -25          34
  • 19           Watford                                                38            -28          34
  • 20           Norwich City                                      38             -49          21

Wasanni

Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta 2023/2024.

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Bayer Leverkusen ta zama zakarar gasar Bundesliga ta shekarar 2023/2024, bayan da suka samu nasara a kan Weder Bremen da ci 5-0.

Hakan ne kuma ya kawo ƙarshen shekaru 11 da Bayern Munich, da ta yi tana lashe gasar.

Wannan dai shi ne karo na farko da Bayer Leverkusen suka taɓa lashe gasar a tarihi, ida suka gaza ɗaukar kofin a shekarar 2002 a ranar ƙarshe ta gasar.

Har ila yau, a dai wannan shekarar ne su kayi rashin nasara hannun Shalke 04, a wasan ƙarshe na German Cup Da ci 4-2.

Haka kuma, Real Madrid suka doke su a wasan ƙarshe na zakarun nahiyar turai.

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar bata taɓa ɗaukar wata gasa ba a ƙarni na 21, sai bayan da Xavi Alonso ya karɓe su.

Continue Reading

Wasanni

Hukumar NPFL, ta amince da buƙatar Kano Pillars na ɗage wasan ta na mako na 28 da Enyimba

Published

on

Yanzu haka an samu dai-daito da hukumar NPFL, wanda ta amince da bukatar Kano Pillars na dage wasanta na mako na 28, da Enyimba zuwa ranar Alhamis, mai zuwa.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, ce ta wallafa hakan a shafin ta na Facebook da yammacin Litinin ɗin nan, ta ce ƴan wasan ta za su tashi a gobe Talata, da safe zuwa Aba domin fafata wasannin su.

Idan dai ba’a manta ba ƙungiyar ta wallafa kaɗan daga irin ƙalubalen da take fuskanta a harkokin gudanarwar ta.

Pillars, ta wallafa ƙalubalen ne kamar haka, “A yanzu haka zancan da muke muku Kano Pillars ta rasa kudin da za taje garin Aba, domin buga wasan hamayya na Nigeria Premier league wato Zobia Classic”.

Wasan dai shine wasa mafi ɗaukar hankali a league din Nigeria baki ɗaya, ku taya mu yadawa dan Allah.

Continue Reading

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Trending