Connect with us

Labarai

Marayu na bukatar tallafi a lokutan sallah – Dakta Auwal

Published

on

Gidauniyar tallafawa marayu da marasa karfi da ke garin Riga Fada a karamar hukumar Kumbotso mai suna Riga Fada Orphan and Less Privilege ta gabatar da taron bai wa marayu da marasa karfi kayan sallah.

Taron wanda ya gudana a garin Riga Fada a ranar Alhamis, daya daga cikin wadanda su ka samu tallafin a zantawar sa da gidan rediyon Dala.

Ya ce, “Na gode a kan yadda kungiyar ta tallafa mana, kuma ina bukatar a siya min keken guragu, domin na samu saukin tafiya, cuta ce wadda ban dade da samun ta ba, an yi maganin amma abun ya faskara”.

Itama wata uwar marayu mai suna Hadiza Al Mustapha wacce ‘ya’yan ta su ka ci gajiyar tallafin, ta ce, “Mun yi farin ciki, Allah ya buda masu, ya kuma basu kwarin gwiwa, an baiwa ‘ya’yan mu yadiddiga a dinke”.

Kazalika, daya daga cikin jagororin kungiyar, Dakta Auwal Riga Fada ya ce, “Mun fahimci akwai yara da yawa da a ka mutu a ka bar su mata da maza, kuma ba su da wadanda za su dauki nauyin su, wadannan yaran idan sallah ta zo su na kaka. Shi yasa mu kaga dacewar mu samar musu kayan sallah da za su fito cikin farin ciki da na su kayan”.

Ya kuma ce, “Mawadata su tuna cewa, wata rana za su mutu, kuma ba su san yadda za su bar iyalan na su ba, don haka idan mutum ya taimaka to shima zai samu wadanda zasu taimaka masa”. A cewar Dakta Auwal

Wakilin mu Abubakar Sabo ya rawaito cewa, yara kimanani arba’in da kuma marasa makarfi biyar ne su ka ci gajiyar tallafin.

 

 

 

 

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending