Connect with us

Labarai

Lokutan da za a yi Sallar Idi a masallatan Kano

Published

on

Lokutan Sallar Idi Babba da za a gudanar a safiyar ranar Juma’a a wasu daga cikin masallatan Juma’a dake jihar Kano.

Masallacin Juma’a na Ibadur Rahaman Tudun Yola layin Attahiru Jega, za a yi sallar Idi da karfe 7:45 na safiya a harabar Masallacin dake Tudun Yola GRA layin Farfesa Attahiru Jega.

Masallacin idi na garin ‘Yankusa a karamar hukumar Kumbotso za ayi Sallah da karfe 8: 00 na safiya

Masjid Sahaba Kundila Maiduguri Road Kano, za a yi Sallar Idi karfe 8:15.

Masallacin Juma’a, (JIBWIS) Wailari, filin Makarantar Wailari Special Pprimary School za a yi tayar da Sallah karfe 8:30.

Masallacin Idi na garin Durba dake karamar hukumar Kibiya za ayi Sallah karfe 8:45 a filin Idi na garin Durba.

Masallacin Jumu’a na Uhud Na’ibawa Zaria Road za a yi Sallah da karfe 8:30.

Masallacin Abubakar Sadeeq dake Dantamashe A Zangon Gabas za a yi Sallah da 8:00 a karamar hukumar Ungogo.

Garin Dandalama dake karamar hukumar Dawakin Tofa za agudanar da sallar idi babba a ranar Juma’a da misalin karfe 8 a filin makarantar Primary dake garin Dandalama.

Masallacin Bilal dake Karkasara Tarauni za a yi Sallah da karfe 8:00.

Masallacin Abdullahi bin Umar Shekar Mai Daki karfe 8:15.

Masallacin Juma’a na Mariri dake karamar hukumar Kumbotso za a yi sallah 8:15.

Masallacin Nurul Anwar Kwaciri karfe 8:30.

Masallacin Juma’a na Sabilur Rashad dake Ibrahim Umar Street, Hausawa Zoo Road, Za a tayar da Sallah karfe 7:45 na safiya.

Masallacin Jumma’a na ZHERA dake rukunin gidajen Kundila Zoo Road, Za a tayar da Sallah karfe 8 na safe.

Masallacin Juma’a na Sheikh Ibrahim A Ramadan Tudun Nufawa karfe 8:15.

Masallacin Juma’a na Kanwa Madobi karfe 8:00.

Masallacin Juma’a na Bechi Kumbotso karfe 8:30.

Masallacin Juma’a na garin Kumbotso za a yi sallah karfe 8:30.

Masallacin Juma’a na Mariya Sunusi Dan Tata dake Danladi Na Sidi karfe 8:00.

Masallacin Juma’a na Ansaruldin karfe 8:00.

Masallacin Sheikh Ibrahim Inyas Gadon Kaya 8:15.

Masallacin Juma’a na Izala dake ‘Yan Shana Kumbotso 8:30.

Masallacin Mash Arul Haram dake Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kumbots za ayi sallah da karfe 8:00.

Masallacin Jauma’a na Abubakar Sadik dake Gwammaja kan titin Tagwayan gida karkashin Liman, Alkali Halhalatul Khuza’i karfe 8:00.

Masallacin Juma’a na Ado Bayero dake garin Ja’en a karamar hukumar Gwale 8:00.

Masallacin Juma’a na Mallam Abubakar Dan Tsakuwa dake Ja’en Ring Road a karamar hukumar Gwale karfe 8:30.

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Hangen Dala

Yau za’a fara Shari’ar Ganduje da gwamnatin Kano

Published

on

A yau ne babbar kotun jaha mai lamba 4 zata fara sauraron wata sharia wadda gwamnatin kano ta ahigar.

 

Gwamnatin jahar kano dai ta shigar da karar tsohon gwamnan jahar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat Umar Ganduje da kuma dansu Umar Abdullahi Ganduje da kuma wani kamfani mai suna Lamash da kuma Dr Jibrilla Muhammad.

 

Gwamnatin jahar kano dai tana zargin Ganduje da wadanna mutane da laifin hada baki da barnatar da dukiyoyin gwamnati.

 

 

Cikin zarge-zargen da ake yiwa su Ganduje akwai batun sun sayar da wasu filotai ba bisa ka’ida ba.

 

 

Da kuma batun zargin da akewa Ganduje na badakalar karbar dala tun a shekarar 2019.

 

 

Yanzu haka an girke jami,an tsaro a harabar sakateriyar Audu Bako inda kuma daga yanzu zuwa kowane lokaci kotun zata fara sauraron korafin kamar yadda wakilinmu Yusuf Nadabo Ismail ya rawaito

Continue Reading

Labarai

Ku tallafawa mazauna gidajen gyaran halin dan rage musu raɗaɗin rayuwa – Mallam Ibrahim Bunkure

Published

on

Limamin masallacin Salafussaleh dake unguwar Ɗorayi ƙarama a jihar Kano, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya shawarci al’umma da su ƙara dagewa wajen tallafawa mazauna gidajen ajiya da gyaran hali, da masu buƙata ta musamman, domin rage musu wani raɗaɗin rayuwa na yau da kullum.

Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya bayyana hakan ne yayin da suka tallafawa mazauna gidan gyaran hali na Goron Dutse, da kayayyakin Abinci, da kuma na gidan yara, a wani ɓangare na taya su bikin ƙaramar Sallah, wajen ganin sun samu farin ciki a bukukuwan ƙaramar sallar da aka gudanar.

Ya ce matuƙar masu hali za su rinƙa tallafawa mazauna gidan gyaran halin da abubuwan da suka sawwaƙa, babu makawa za’a rage musu wata damuwa ta yau da kullum.

Wakilinmu Yakubu Ibrahim Dogarai ya rawaito cewa, Mallam Ibrahim Abdullahi Bunkure, ya ce daga cikin kayan abincin da suka kai wa mazauna gidajen akwai Tuwon Sallah, da garin Kwakwaki, da kuma sinadarin Ɗanɗano, da Sukari, domin ragewa mazaunan gidajen wani raɗaɗin rayuwa.

Continue Reading

Trending