Connect with us

Labarai

Lokutan da za a yi Sallar Idi a masallatan Kano

Published

on

Lokutan Sallar Idi Babba da za a gudanar a safiyar ranar Juma’a a wasu daga cikin masallatan Juma’a dake jihar Kano.

Masallacin Juma’a na Ibadur Rahaman Tudun Yola layin Attahiru Jega, za a yi sallar Idi da karfe 7:45 na safiya a harabar Masallacin dake Tudun Yola GRA layin Farfesa Attahiru Jega.

Masallacin idi na garin ‘Yankusa a karamar hukumar Kumbotso za ayi Sallah da karfe 8: 00 na safiya

Masjid Sahaba Kundila Maiduguri Road Kano, za a yi Sallar Idi karfe 8:15.

Masallacin Juma’a, (JIBWIS) Wailari, filin Makarantar Wailari Special Pprimary School za a yi tayar da Sallah karfe 8:30.

Masallacin Idi na garin Durba dake karamar hukumar Kibiya za ayi Sallah karfe 8:45 a filin Idi na garin Durba.

Masallacin Jumu’a na Uhud Na’ibawa Zaria Road za a yi Sallah da karfe 8:30.

Masallacin Abubakar Sadeeq dake Dantamashe A Zangon Gabas za a yi Sallah da 8:00 a karamar hukumar Ungogo.

Garin Dandalama dake karamar hukumar Dawakin Tofa za agudanar da sallar idi babba a ranar Juma’a da misalin karfe 8 a filin makarantar Primary dake garin Dandalama.

Masallacin Bilal dake Karkasara Tarauni za a yi Sallah da karfe 8:00.

Masallacin Abdullahi bin Umar Shekar Mai Daki karfe 8:15.

Masallacin Juma’a na Mariri dake karamar hukumar Kumbotso za a yi sallah 8:15.

Masallacin Nurul Anwar Kwaciri karfe 8:30.

Masallacin Juma’a na Sabilur Rashad dake Ibrahim Umar Street, Hausawa Zoo Road, Za a tayar da Sallah karfe 7:45 na safiya.

Masallacin Jumma’a na ZHERA dake rukunin gidajen Kundila Zoo Road, Za a tayar da Sallah karfe 8 na safe.

Masallacin Juma’a na Sheikh Ibrahim A Ramadan Tudun Nufawa karfe 8:15.

Masallacin Juma’a na Kanwa Madobi karfe 8:00.

Masallacin Juma’a na Bechi Kumbotso karfe 8:30.

Masallacin Juma’a na garin Kumbotso za a yi sallah karfe 8:30.

Masallacin Juma’a na Mariya Sunusi Dan Tata dake Danladi Na Sidi karfe 8:00.

Masallacin Juma’a na Ansaruldin karfe 8:00.

Masallacin Sheikh Ibrahim Inyas Gadon Kaya 8:15.

Masallacin Juma’a na Izala dake ‘Yan Shana Kumbotso 8:30.

Masallacin Mash Arul Haram dake Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kumbots za ayi sallah da karfe 8:00.

Masallacin Jauma’a na Abubakar Sadik dake Gwammaja kan titin Tagwayan gida karkashin Liman, Alkali Halhalatul Khuza’i karfe 8:00.

Masallacin Juma’a na Ado Bayero dake garin Ja’en a karamar hukumar Gwale 8:00.

Masallacin Juma’a na Mallam Abubakar Dan Tsakuwa dake Ja’en Ring Road a karamar hukumar Gwale karfe 8:30.

Labarai

Gwamnatin Kano za ta inganta filaye da bunƙasa duk ɓangarorin wasannin matasa – Kwamishinan Matasa da Wasanni

Published

on

Sabon kwamishinan ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa na Jihar Kano Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya bada tabbacin cewar Gwamnatin Jihar za ta ɗauki matakin inganta filayen tare da bunƙasa duk wasu ɓangarorin wasanni da matasa ke yi.

Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne yayin da ya kama aiki yau Asabar, tare da kai ziyara a wasu filayen wasannin dake ihar Kano.

Daga cikin filayen wasannin da ya ziyarta akwai filin wasa na Sani Abacha da ke ƙofar Mata, da filin wasa na Kano Pillars da ke sabon Gari, da kuma filin wasa na Ado Bayero Square dake unguwar Sabon Gari, sai kuma filin wasa na Mahaha da ke ƙofar Na’isa.

Da yake jawabi bayan kammala ziyarar kwamishinan wasannin da ci gaban Matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa kwankwaso, ya ce ya gudanar da ziyarar ce domin sanin halin da filayen wasannin ke ciki.

A lokacin ziyarar kwamishinan na tare da mai bai wa Gwamnan Kano shawara a kan harkokin wasanni Ambasada Yusuf Imam Ogan Ɓoye, da shugaban magoya bayan ƙungiyar ƙwallon Ƙafa ta Kano Pillars Alhaji Rabi’u Abdullahi Kawo, da kuma mai riƙon Shugabancin hukumar wasanni ta jiha Malam Bala Sani Shehu.

Continue Reading

Labarai

Muna sane da ƙarancin Ruwa a wasu sassan Kano – Hukumar rarraba ruwan Sha

Published

on

Hukumar rarraba ruwan sha ta jihar Kano ta ce matsalar rashin samun ruwa da ake fuskanta a wasu sassan jihar Kano, yana da alaƙa ne da lalacewar wani abun kan Famfo a madatsar ruwan da ke Tamburawa.

Shugaban hukumar Injiniya Garba Ahmad Bichi, ne ya bayyana haka yayin zantawar sa da manema labarai, ya ce cikin guraren da za’a yiwa gyaran har da madatsar ruwa ta Challawa da Watari, da amincewar gwamnatin jihar Kano.

Injiniya Garba, ya kuma ce suna sane da ƙarancin ruwan da ake fuskan ta a wasu sassan jihar Kano, amma nan gaba kaɗan za kammala gyaran kan famfon, domin ganin an wadata sassan jihar Kano, da ruwan domin ganin sun samu wani sauƙi.

 “Mu ma a ɓangaren mu Bama jin daɗin yadda al’umma suke rasa ruwa a sassan jihar Kano, kuma nan da ranar Litinin mutane za su fita daga cikin wannan matsala ta rashin Ruwa, a yanku nan su, “in ji shi”

Garba Ahmad, ya kuma ƙara da cewa matsalar fashewar Fayif da aka samu a ci gaba da aikin gadar mahaɗar Ɗan Agundi, yanzu haka suna kan ɗaukar mataki tsakanin su da kamfanin da suka taka har ya fashe, dan ganin an gyara al’ummar da ake baiwa ruwa su ci gaba da damu.

Continue Reading

Labarai

Ƴan kasuwa ku tsaftace magudanan ruwa bisa gabatowar Damuna – Ƙungiyar Amata ta kasuwar Singa

Published

on

An buƙaci ƴan kasuwa da su rinƙa tsaftace tare da gyara magudanan ruwa a cikin kasuwannin su, bisa yadda damuna ke ƙara gabatowa.

Shugaban ƙungiyar Amata reshen kasuwar Singa Alhaji Musa Ibrahim Ɗan gaske, ne ya bukacin hakan a zantawar sa da manema labarai, yayin kaddamar da tsaftace kasuwar da kuma gyara mugudanun ruwan kasuwar.

Alhaji Musa, ya kuma ce ta hanyar tsaftace magudanan ruwan ne za a gujewa kowacce irin ambaliyar ruwa a cikin kasuwanni.

Continue Reading

Trending