Connect with us

Wasanni

Guardiola: Liverpool ta dagulamin lisafi a rayuwa ta

Published

on

Mai horas da Manchester City, Pep Gurdiola ya ce haduwa da Jurgen Klopp da kuma Liverpool su ne babban kalubalen da ya taba fuskanta a aikin horaswar sa.

Pep na wannan furucin ne bayan da Liverpool ta lashe gasar a karo na farko ta kuma baiwa Manchester City tazarar maki 18 a tsakanin juna.

Ya ce”Na san Klopp tun ina Bayern shi kuma ya na Dortmund, domin kuwa yanzu sai da ya sa Liverpool ta mamaye komai wajen lashe kyaututtuka, wanda Liverpool ta zama babban kalubale a matsayin abokiyar hammayar da na taba hanuwa da ita, su na da nagarta da jajurtattun ‘yan wasan dole na ce Liverpool ta bani wahala a iya tsawon rayuwa ta na horaswa. Duk da cewa Real Madrid ta na da karfi kuma ta tallafa mun na zama babban mai horaswa a lokacin Jose Mourinho da kuma Pellegrini. Idan ka tambayeni wacce kungiya ce ta fi ban wahala da na tunkara, zan iya cewa Liverpool ce, saboda farkon da na zo kasar Ingila sai da Liverpool ta zama babban kungiya da ta fi Real Madrid karfi”. Pep

Liverpool ta zama zakara a kasar Ingila a karo na faro tun cikin shekaru 30 wanda ta lashe Firimiya da tazarar maki 18 a tsakanin na daya da na biyu.

Wasanni

Glesner ya zama sabon mai horas da Palace.

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace ta sanar da nadin Oliver Glesner a matsayin sabon mai horaswar ta.

Glesner wanda tsohon mai horas da kungiyar kwallon kafa ta Eintracht Frankfurt ne mai shekaru 49 dan asalin kasar Austrian, ya maye gurbin tsohon mai horaswa Roy Hodson, wanda ake ganin ya gaza kai kungiyar ga tudun mun tsira.

A wasanni 16 da Crystal Palace ta buga a bayan nan ta yi rashin nasara a wasanni 10 duk karkashin jagorancin Roy Hodson wanda hakan yasa take mataki na 16 a teburin gasar firimiyar kasar Ingila.

Glesner dai ya rattaba kwantaragi da Palace har na tsawon shekaru biyu, zai kuma jagoranci kungiyar a wasan sa na farko da kungiyar kwallon kafa ta Burnley a ranar Asabar mai kamawa.

Continue Reading

Wasanni

Kasar Cote D’Ivoire ta yi nasara akan Najeriya 2-1, a gasar nahiyar Afrika ta Afcon 2023.

Published

on

Kasar Ivory Coast ta lashe gasar cin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) na 2023, bayan doke Najeriya da ci 2 da 1 a wasan karshe na gasar.

Rahotanni dai sun bayyana cewar mai masaukin bakin ta zama zakara ne, bayan ta warware kwallon da Najeriya ta jefa mata kafin tafiya hutun rabin lokaci a raga.

Yayin wasan dai dan wasan bayan Najeriya, Troost Ekoong ne ya fara jefa mata kwallo a minti na 38 a ragar Ivory Coast.

Sai dai kuma bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Ivory Coast ta warware kwallon a minti na 62 ta hannun dan wasan tsakiyarta, Franck Kessie.

Yayin da aka kai munti na 81 Sebastian Haller ya kara wa mai masaukin baki kwallo ta biyu a raga, wanda hakan ya sanya ta zama zakarar AFCON ta 2023.

Yanzu haka dai ana shirye-shiryen bayar da kyauta ga kasar da ta yi nasara, da kuma wadanda aka shirya baiwa kyaututtukan, wanda kuma a wajen yanzu haka akwai mataimakin shugaban kasa Kasheem Shatima, da gwamnan jihar Katsina Umar Dikko Radda, da na jihar Nassarawa Abdullahi Sule, da kuma ministan Wasanni, da sauransu.

Idan ba a manta ba Najeriya ta doke Ivory Coast a wasan rukuni da suka fafata da ci daya ta hannun Troost Ekoong a bugun fanareti, kamar yadda jaridar Aminiya ta rawaito.

Continue Reading

Wasanni

Afcon2023: Ivory Coast za ta kara da Mali da yammacin yau Asabar

Published

on

A ci gaba da gasar cin kofin nahiyar Africa da ake fafatawa a kasar Cotdebua, a Asabar din nan ne tawagar masu masaukin baki Ivory Coast, za su fafata da kasar Mali, domin samun damar tsallakawa zagaye na daf da karshe a gasar.

Za dai a take wasan ne da misalin 6 na yamma yau, a filin wasa na Stade De Bouake.

Hakasalika suma kasar Cape Verd, za su kara da tawagar kasar Africa ta kudu a filin wasa na Stade Charles Konan Banny, da misalin karfe 9 na daren yau Asabar.

Ko a jiya ma dai wasan da aka buga tsakanin Najeriya da Ango, Super Eagle tayi nasara akan Ango da ci daya ba ko daya.

Continue Reading

Trending