Connect with us

Ilimi

MKG: Ta shuka bishiyoyi domin dakile kwararowar Hamada a Kano

Published

on

Gamayyar matasan Kano da ke gangamin dasa bishiyoyi a jihar Kano (Make Kano Green) ta dasa Bishiyoyi 1,567 a kananan hukumomi biyar a jihar.

Babban jami’I a kungiyar, Isma’il Auwal ne ya bayyana hakan, a ganawar sa da Dala FM ranar Lahadi, lokacin da su ke ci gaba da shuka Bishiyoyi a yankin Yalwa dake unguwar Mariri a karamar hukumar Kumbotso.

A cewar sa” Mun samu hadin kan al’umma, wajen gudanar da gangamin dashen Bishiyoyin, haka kuma mu na bibiyar dukkanin wuraren da mu ka dasa shuka, domin ganin halin da suke ciki a lokaci da kuma bayan lokaci”.

A nasa bangaren mai unguwar Yalwa, Alhaji Abdullahi Shehu ya ce,” Mun yi farin ciki da wannan gangami, sannan na yi alkawarin yin shiri na musamman, domin kula da bishiyoyin da a ka dasa wajen ganin ba su lalace ba”.

Sai dai irin wannan yunkuri da matasan ke yi, na fuskantar barazana, musamman daga masu dabi’ar saran itace, wadanda mafi yawa na kallon yunkurin yaki da kwararowar hamada matsayin kamar wasa ne zancen.

Haka kuma mafi yawan ‘yan Nijeriya na sare Bishiyoyi, duk da dimbin iskar Gas da kasar ke da ita.

Kwamaret Sani Musa Idris, wani dan gwagwarmaya ne mai fafutukar kare muhalli a Kano, ya ce”Akwai bukatar kara zage damtse wajen yin dashen Bishiyoyin, domin magance matsalar kwararowar hamada”.

Wakilin mu Bashir Sani Abubakar ya rawaito cewa ko a shekarar 2010, hukumar raya al’adun Birtaniya da hadin gwiwar hukumar raya gandun daji ta jihar Kano, sun gabatar da wani shirin yin dashe a jihar, domin magance kwararowar Hamada, wanda su ka dasa bishiyoyi dubu takwas a wancan lokaci.

Ilimi

Kaduna:- Daliban Kuriga sun sha ki iskar ‘yanci

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da rahoton cewa an sako duka ɗaliban makarantar Kuriga da ƴanbindiga suka sace.

 

An sace ɗaliban firamare da na sakandare su kusan 287 a makarantarsu da ke ƙauyen Kuriga a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna fiye da makonni biyu da suka wuce.

 

Sanarwar da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya fitar ta ce an sako duka ɗaliban kuma suna cikin koshin lafiya.

 

Sanarwar ba tayi karin bayani ba game da irin matakan da aka bi wajen sako ɗaliban, sai dai gwamna Uba Sani ya nuna godiya ga shugaba Tinubu da mai bashi shawara kan tsaro da kuma sojojin Najeriya saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an sako ɗaliban.

 

“Ba dare babu rana ina tattaunawa da Malam Nuhu Ribadu domin lalubo hanyoyin da za a bi wajen kubutar da daliban, kafin mu samu nasara,” in ji Uba Sani.

 

Galibinsu ɗaliban da aka sace ƴan shekaru biyar ne zuwa 18.

Continue Reading

Hangen Dala

Gaya Ajingi Albasu:- Dan majalisa ya raba kayan abinci

Published

on

Dan majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu Dakta Ghali Mustafa Fanda ya fara rabon tallafin kayan abinci ga al’ummar kananan hukumomin uku.

 

Yayin rabon tallafin kayan abincin, Dakta Ghali Mustafa yace yayi rabon tallafin ne domin fara sauke nauyin al’ummar da yake wakilta.

 

” Wannan tallafi zamu bayar da shi ne domin fara sauke nauyin al’ummar da suka zabe mu, kuma wannan shi ne karon farko, kuma yayi daidai da bukatar al’umma a yanzu, shiyasa muka fara da tallafin kayan abinci”.

 

“A cikin wannan tallafi mutane kimanin dubu ashirin ne zasu amfana, wanda zamu bayar da buhunan Shinkafa da Gero da Garin masara.”

 

Haka kuma ɗan majalisar ya bayar da tallafin Naira miliyan ashirin ga matasan kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu.

 

Sai kuma ɓangaren dalibai mata, wanda shima a yau dan majalisar ya dauki nauyin karatun dalibai mata guda 60 a bangaren lafiya.

 

Haka kuma cikin jawabin nasa Hon Ghali ya kuma ce nan gaba kadan zai bayar da tallafin taki ga manoma, da kuma farfaɗo da dukkanin rijiyon burtsatse na kananan hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu a wani mataki na samar da ruwan sha.

 

Da yake nasa jawabin mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam Gwarzo wanda ya samu wakilcin mai baiwa Gwamna Shawara kan harkokin siyasa Hon Sunusi Surajo Kwankwaso kira yayi ga sauran wakilan al’umma da suyi koyi da Dakta Ghali Mustafa Fanda wajen ayyukan alkhairi da kuma jin kan al’umma.

 

Haka kuma Hon Sunusi Surajo ya yabawa dan majalisar bisa bayar da tallafin ga ƙananan hukumomin uku.

 

Taron dai wanda ya gudana a cikin Islamic Centre na karamar hukumar Gaya ya samu halartar manya, da kuma jagororin yankunan uku, kuma nan take Dan majalisar Tarayya Dakta Ghali Mustafa ya fara rabon tallafin

Continue Reading

Ilimi

Za’a daga likafar BMC zuwa Diploma – Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin Kano tace nan bada jimawa ba za’a daga likafar makarantar koyon aikin jarida a matakin farko wato BMC ta Goron Dutse zuwa tsarin Diploma.

Mataimakin gwamnan Kano Kwamred Aminu Abdussalam ne ya tabbatar da hakan lokacin da yake jawabi a wurin taron da kungiyar tsaffin daliban makarantar suka shirya.

Kwamred Aminu Abdussalam ya kuma ce nan bada jimawa ba makarantar za’a daga matsayin karatun daga Certificate zuwa Diploma, kamar yadda makarantar ta bukata.

Kazalika yace gwamnatin Kano za ta cigaba da lura da dukkanin kayan koyo da koyarwa har ma da ababen hawa na hukumar ilimin manya ta Kano, wato Agency for mass Education wadda a cikin ta ake karatun na jarida.

Taron dai wanda shi ne karo na farko da gamayyar kungiyar daliban ta shirya tun bayan kafuwar makarantar shekaru 38 da ta gabata, ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka haɗar da Kwamishinan ilimi na Kano da Kwamishinan yada labarai da kwamishiniyar mata da mai baiwa gqamna shawara kan harkokin yada labarai.

Kazalika taron ya samu halartar Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da tsaffin malaman makarantar da kuma shugabannin kafafen yada labarai na Kano.

A yayin taron dai shugaban kungiyar taaffin daliban Ismaila Ammai me Zare ya kaddamar da wani tsari na tallafawa makarantar da abin zama mai taken ( ka dawo da kujerar ka ).

Continue Reading

Trending