Koma Labarai
Tattalin Arziki

Da Ɗumi-Ɗumi: Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin ƙaramin ministan kuɗi

Hassan Mamuda Ya'u 0 views
Da Ɗumi-Ɗumi: Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin ƙaramin ministan kuɗi

Shugaban Najeriya, Bola Ahmad Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin sabon ƙaramin ministan kuɗi na ƙasar, jim kaɗan bayan da Majalisar dattawa ta tantance shi a matsayin minista a gwamnatin tarayyar ƙasar.

Kafar DCL Hausa ta ruwaito cewa, Shugaba Tinubu, ya amince da naɗinsa a matsayin karamin minista a ma'aikatar kudi ta Nijeriya.

Kafin naɗin nasa a wannan muƙamin shi ne Mai taimaka wa Tinubu kan harkokin haraji na gwamnatin Najeriya.

Ready to PlayDala FM88.5 FM