Koma Labarai
Siyasa

Da Ɗumi-Ɗumi: Gwamnatin Kano ta rushe ma'aikatar ilimi mai zurfi a jihar

0 views
Da Ɗumi-Ɗumi: Gwamnatin Kano ta rushe ma'aikatar ilimi mai zurfi a jihar

Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya amince da rushe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi (Ministry of Higher Education) tare da haɗe ta da Ma’aikatar Ilimi.

Gwamnatin jihar ta ce wannan wani mataki ne da gwamnatin ta ce zai kara inganta tsari da saurin aiwatar da sauye-sauye a bangaren ilimi.

Bayanin hakan na ƙunshe ne a cikin sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi 15 ga Maris, 2026.

Sanarwar ta ce bayan wannan sauyi, sabon tsarin zai ci gaba da aiki da sunan Ma’aikatar Ilimi, inda za a kafa Sashen Ilimi Mai Zurfi (Directorate of Higher Education) a karkashinta domin kula da harkokin jami’o’i da sauran manyan cibiyoyin ilimi a jihar.

Sanarwar ta kara da cewa dukkan hukumomin da ke karkashin tsohuwar ma’aikatar, ciki har da Hukumar Ba da Tallafin Karatu (Scholarship Board), za su koma karkashin Ma’aikatar Ilimi, yayin da jami’o’in gwamnati da sauran manyan makarantu za su kasance ƙarƙashin sabon sashen.

Ready to PlayDala FM88.5 FM