A karon farko: Iran da Saudiyya sun tattauna tun bayan fara yaƙin Gabas ta Tsakiya
Hassan Mamuda Ya'u 0 views

Rahotanni sun bayyana cewa, Ministan harkokin wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan Al Saud, ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na Iran, Abbas Araqchi, a karon farko tun bayan ɓarkewar yaƙi da hare‑haren Iran a yankin Gabas ta Tsakiya.
Ma’aikatar harkokin wajen Saudiyya ta bayyana a shafin ta na X cewa, ministocin biyu sun tattauna kan sabbin abubuwan da suka faru a yankin, tare da bincikar hanyoyin rage tashin hankali don dawo da tsaro da kwanciyar hankali a yankin
Majiyoyi sun bayyana cewa wannan shi ne mataki na farko na hulɗa kai tsaye a tsakanin ƙasashen biyu a cikin wannan rikici da ake yi, kamar yadda kafar BBC ta ruwaito.



