Koma Labarai
Shari'a

Za a hukunta duk lauyan gwamnati da bai fito aiki ba - Ma'aikatar shari'a a Kano.

Hassan Mamuda Ya'u 0 views
Za a hukunta duk lauyan gwamnati da bai fito aiki ba - Ma'aikatar shari'a a Kano.

Hukumar gudanarwa ta ma'aikatar shari'a ta jihar Kano, ta bayyana cewar za a hukunta duk lauyan da bai fito aiki a gobe Laraba ba.

Hakan na cikin sanarwar da hukumar ta fitar a cikin daren Talata 10 ga watan Maris, 2026.

Hukumar gudanarwar ta bayyana cewar tun daga kan daraktoci har zuwa kan ƙananun ma'aikata ba a ɗauke wa kowa zuwa aiki ba.

Wakilin Dala FM Kano, Yusuf Nadabo Isma'il ya ruwaito cewa, hukumar ta kuma ce bijirewa sanarwar dai-dai ta ke da saɓawa dokar ɗauka da ladabtar da ma'akaci.

Hakan na zuwa ne a dai-dai lokacin da ƙungiyar lauyoyin gwamnati reshen jihar Kano, ke shirin shiga yajin aikin sai baba ta gani, sakamakon jan ƙafa a kan haƙƙoƙinsu da suka maƙale a ma'aikatar.

Ready to PlayDala FM88.5 FM