Adeleke ya sake lashe zaɓen gwamnan jihar Osun karo na biyu.
Hassan Mamuda Ya'u 0 views

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa INEC ta ayyana Ademola Adeleke, wanda ya tsaya takara a ƙarƙashin jam'iyar Accord, a matsayin wanda ya lashe zaɓen.
Ademola Adeleke dai ya samu ƙuri’u 511,067, yayin da Oyebamiji na jam'iyyar APC ya samu ƙuri'u 444,815.
Ya samu nasarar ne a ƙananan hukumomi 19 daga cikin 30, yayin da Oyebamiji na APC ya lashe guda 11.
Wannan nasara ta ba Adeleke damar komawa kujerar gwamnan Osun na wa’adi na biyu.
A ranar Asabar 15 ga watan Agusta, 2026, ne dai aka gudanar da zaɓen gwamnan jihar Osun.



