Koma Labarai
Labarai

Za a gurfanar da duk wanda yaci mutuncin gwamnan Kano, ko wani mutum a kotu - Gwamnatin Kano

Hassan Mamuda Ya'u 0 views
Za a gurfanar da duk wanda yaci mutuncin gwamnan Kano, ko wani mutum a kotu - Gwamnatin Kano

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewar za ta gurfanar da duk wani mutum da aka kama da laifin cin mutuncin mutane, a dai-dai lokacin da wasu matasa su ke yi wa gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ɗan kira.

Kwamishinan shari'a na jihar Kano, Barrister Abdulkarim Maude SAN, ne ya bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai da ya gudana a ranar Juma'a ma'aikatar sharia ta jihar Kano.

Kwamishinan ya bayyana cewar doka ta yarda da faɗin albarkacin baki amma ba ta yadda da cin mutunci ba.

A cewar sa, "Za mu gurfanar da duk wani mutum da masu bincike suka samu da laifi a kan sa a gaban kotu, in ji shi.”

Wakilinmu Yusif Nadabo Isma'il ya ruwaito cewa, jawabin kwamishinan na zuwa ne dai-dai lokacin da wasu matasa suke yi wa gwamnan kano ɗan kira a kan hanya.

Ready to PlayDala FM88.5 FM