Koma Labarai
Labarai

Sarkin Kano ya hori dagatai 3 da ya naɗa da su zauna lafiya da al'ummar su.

Hassan Mamuda Ya'u 0 views
Sarkin Kano ya hori dagatai 3 da ya naɗa da su zauna lafiya da al'ummar su.

‎‎‎Mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu, ya naɗa sabbin dagatai guda uku da suke daga yankin gundumar Kunya a karamar hukumar Minjibir, inda aka naɗa Shamsu Aminu a matsayin dagacin Garke, da Abdulhamid Muhammad a matsayin dagacin garin Tsage.

Sarkin ya kuma naɗa Malam Nadabo Lawan a matsayin dagacin garin dogon kawo da ke ƙaramar hukumar Doguwa.

‎Bayan kammala naɗin nasu ne mai maraba sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu, ya hore su da su zauna lafiya da al'ummarsu, tare da sanya idanu a kan harkokin tsaro da lafiya da ilimi a garuruwansu.

Da yake jawabi dagacin garin Dogon Kawo a ƙaramar hukumar doguwa Malam Nadabo Lawan, ya bayyana farin cikinsa bisa naɗashi da mai maraba sarkim na Kano Khalifa Muhammadu Sanusi II ya yi a matsayin dagacin.

Ya kuma ce zai gudanar da aikinsa bisa gaskiya da rikon amana tare da kira ga al'ummar garin nasa da su ba shi haɗin kai da goyon baya a kowane lokaci.

‎Wakilinmu na masarautar Kano Shamsu Da'u Abdullahi ya rawaito cewa, al'umma daban-daban daga ƙananan hukumomin Kano sun halarci taron naɗin dagatan da ya gudana ranar Alhamis, a fadar masarautar Kano.

Ready to PlayDala FM88.5 FM