Kotu ta wanke Hafizin Alqur'ani, Ja'afar bisa rashin samun sa da laifin satar wayar dubu 19 a Kano.
Hassan Mamuda Ya'u 0 views

Kotun majistiri da ke zamanta a Ƙaramar Hukumar Kura a jihar Kano, ta wanke Hafizin Alqur'ani, Ja'afar Abdullahi Ishaq, bisa rashin samun sa da laifin satar wayar salula ta naira dubu 19.
Kafin wanke shi, Ja'afar Abdullahi ya shafe makonni 3 yana tsare a gidan ajiya da gyaran hali a Kano.
Alkalin Kotun, Mai Shari'a Muhammad Alhaji Isa, ya wanke Ja'afar ne bayan dogon nazari da kuma bincike a kan shari'ar.
Tunda farko dai an zargi Malam Ja'afar da ƙwace wayar wani yaro da aka aika ya kai Caji a Garin Rantan na Ƙaramar Hukumar Bebeji.
Kafar GTR Hausa ta ruwaito cewa, kotun ta sallami Ja'afar Abdullahi ne bayan da ta gano cewa sharri aka yi masa.



