Za mu mara baya ga duk ƙungiyar da ke son kawo ci gaba a Kano - Sarkin Kano

Mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu, ya bayyana cewa masarautar Kano shirye take wajen marawa duk wata ƙungiya baya da za ta kawo cigaba a faɗin jihar Kano.
Sarkin ya bayyana hakan ne a yayin ƙaddamar da ƙungiyar ƙwararrun sakatarori ta ƙasa da kuma reshen ta na Kano, wanda aka gudanar yau Alhamis 11 ga Yuni, 2026, a Kano.
Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu ya kuma bayyana jihar Kano da cewa, cibiyar kasuwanci ce a fadin Afrika, inda ya kuma taya ƙungiyar murna bisa cikar ta shekara sintin da kafuwa.
A nasa jawabin, sabon shugaban Ƙungiyar sakatarori da ƙwararru a aikin gwamnati ta ƙasa ICSAN, reshen jihar Kano, Barista Muhammad Na Sambo, ya yi alkawarin kawo cigaban da ya dace a ƙungiyar da ma jihar Kano.
Wakilinmu na masarautar Kano Shamsu Da'u Abdullahi ya rawaito cewa, Farfesa Kamilu Sani Fagge da Farfesa Abdulmuminu Ahmed daga jami'ar bayero ne suka gabatar da mukala a wajen taron, wadda ta ƙunshi harkokin cigaban Kasuwanci a jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.



