Da Dumi-Dumi: Sojoji sun dakile yunkurin satar ɗalibai mata a jihar Borno
Hassan Mamuda Ya'u 0 views

Dakarun sojin Nijeriya karkashin shirin 'Operation Hadin Kai' sun samu nasarar dakile wani yunƙuri na sace ɗalibai a kwalejin tarayya ta mata da ke Monguno a jihar Borno.
Sojojin sun kuma ceto ɗalibai 46, a yayin artabun da suka yi da ƴan bindiga, kamar yadda kafar DCL Hausa ta ruwaito.



