Ƙasa ba za ta samu zaman lafiya mai ɗorewa ba idan miliyoyin jama'arta na rayuwa cikin talauci - Sarkin Kano

Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, ya bayyana cewa ba za a iya magance matsalolin tsaro da ƙasar nan ke fuskanta ta hanyar amfani da ƙarfin soja kaɗai ba, yana mai jaddada cewa samar da tsaron ɗan adam shi ne tushen tabbatar da tsaron ƙasa.
Sarkin ya bayyana hakan ne a yayin da ya gabatar da muhimmin jawabi a matsayin Babban Baƙo mai Jawabi a Babban Taron Ƙasa kan Zaman Lafiya da Tsaro da aka gudanar a Abuja.
A cikin jawabin nasa mai taken "Tsaron Ɗan Adam Shi ne Tsaron Ƙasa", Sarkin ya ce matsalolin da suka haɗa da rashin aikin yi, da talauci, da rashin adalci, da kuma ƙarancin abinci, da sauyin yanayi da kuma raguwar amincewar jama'a ga hukumomi, su ne manyan abubuwan da ke haddasa rashin tsaro a ƙasar.
Ya bayyana cewa matsalar tsaro ta bambanta daga yanki zuwa yanki, inda ya ce a Arewa maso Gabas talauci ne ya haifar da matsalar, a Arewa maso Yamma kuwa ƙarancin shugabanci da yunwa ne suka ƙara ruruta rikicin. Haka kuma a yankin Tsakiya rikicin filaye da sauyin yanayi ne ke haddasa tashin hankali, yayin da a Kudu maso Gabas da yankin Neja Delta ake fama da matsalolin rashin aikin yi, rashin adalci, gazawar shugabanci da kuma ware jama'a daga tattalin arziki.
Khalifa Muhammadu Sanusi II ya kuma jaddada cewa, ƙasa ba za ta samu zaman lafiya mai ɗorewa ba idan miliyoyin jama'arta na rayuwa cikin talauci, yana mai cewa ci gaban tattalin arziki da walwalar jama'a su ne ginshiƙan tsaro na gaskiya.
Wakilinmu na fadar Sarkin Kano Shu'aibu Ubale Minshawi ya ruwaito cewa, taron ya samu halartar manyan jami'an gwamnati da na tsaro, ciki har da tsohon Kwanturola Janar na Hukumar Kula da Shige da Fice, Muhammad Babandede, da Mataimakin Shugaban Ma'aikatan Fadar Gwamnatin Tarayya wanda ya wakilci Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, da gwamnoni, da kuma shugabannin hukumomin tsaro da sauran manyan baƙi daga sassa daban-daban na ƙasar.



