Koma Labarai
Labarai

Sarkin Gumel Dr. Ahmad III, ya rasu a ƙasar Masar yana da shekaru 84.

Hassan Mamuda Ya'u 0 views
Sarkin Gumel Dr. Ahmad III, ya rasu a ƙasar Masar yana da shekaru 84.

Rahotannin da ke fitowa na bayyana cewa, Mai martaba Sarkin Gumel, Dr. Ahmad Muhammad Sani III, ya rasu a yau, Alhamis, 3 ga Satumba, 2026.

Sarkin ya rasu ne bayan ya shafe sama da shekaru 45 yana mulki a masarautar Gumel.

Alhaji Ahmad Muhammad Sani, ya hau gadon sarautar Gumel ne a shekarar 1981, inda ya zama sarki na 16 na masarautar.

Ana sa ran za a sanar da jana’izarsa nan ba da jimawa ba.

Ready to PlayDala FM88.5 FM