Koma Labarai
Labarai

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya soki yadda ake tafiyar da shari’ar El-Rufa'i a kotu

Hassan Mamuda Ya'u 0 views
Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya soki yadda ake tafiyar da shari’ar El-Rufa'i a kotu

Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, ya bayyana damuwarsa kan yadda ake gudanar da shari’ar tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, yana mai cewa dole ne a tabbatar da adalci da bin ƙa’ida ba tare da nuna bambanci ba.

Sarkin ya bayyana haka ne lokacin da yake gabatar da Maƙala a babban taron masu ruwa da tsaki na ƙasa, inda ya yi nuni da cewa akwai buƙatar a mutunta haƙƙin duk wanda ake tuhuma, ciki har da damar samun beli kamar yadda doka ta tanada, yana mai cewa hakan na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da gaskiya a tsarin shari’a.

Ya kuma bayyana El-Rufai a matsayin misali da ya nuna cewa dole ne a riƙa tafiyar da shari’o’i cikin gaskiya, nesa da duk wani abin da zai iya nuna son rai ko tauye haƙƙin ɗan Adam.

A cewarsa, tsarin shari’a mai ƙarfi shi ne wanda ke kare haƙƙin kowa tare da tabbatar da cewa ana bin doka yadda ya kamata ba tare da wariya ba.

Ready to PlayDala FM88.5 FM