Koma Labarai
Tsaro

Matasan da suka yi yunƙurin kashe 'yan Bijilante uku sun shiga hannun rundunar KOSSAP a Kano.

Hassan Mamuda Ya'u 0 views
Matasan da suka yi yunƙurin kashe 'yan Bijilante uku sun shiga hannun rundunar KOSSAP a Kano.

Rundunar tsaro da ke yaki da fadan daba, ƙwacen waya da kuma dakile ta'ammali da kayan maye ta Anti-Phone Snaching Force Kano, ta kama wasu matasa uku bisa zarginsu da yunkurin kashe jami'an kungiyar sintirin Bijilante su uku a Bechi Gunkawa, da ke karamar hukumar Kumbotso a Kano.

Jami'in hulda da jama'a na rundunar ta KOSSAP, a Kano, Ibrahim Garba Ahmad, ne ya bayyana hakan yayin zantawar sa da gidan rediyon Dala FM, a ranar Lahadi 22 ga watan Maris, 2026.

Ibrahim Garba, ya ce da fari guda daga cikin matasan mai suna Shu'aibu Muhammad mai shekaru 20 ne, aka yi zargin ya daki mahaifinsa Mallam Muhammad, lokacin da fada ya kaure tsakanin mahaifin nasa da mahaifiyar sa a gida inda ya shigar wa mahaifiyar tasa fadan.

A cewar sa, ''Bayan faruwar hakan ne Malam Muhammad, ya sanar da jami'an Bijilante na yankin Bechi Gunkawa, inda suka ladaftar da shi, bayan sun sake shi ne ya ja zugar abokansa su hudu inda su ka je gidan 'yan bijilanten rike da makamai suka yi barazanar kashe su sai dai basu samu nasarar hakan ba daga karshe aka kama su, in ji shi."

Ibrahim Garba, ya kuma ce lokacin da suka je kama matasan daya ya tsere inda suka kama uku ciki har da jagoran tawagar, kuma tuni suka amsa laifin da ake zargin su da aikata wa.

Da yake nasa jawabin guda daga cikin jami'an Bijilanten da matasan suka yi yunkurin kashe wa, mai suna Maharazu Abdulmalik, ya ce bukatar su shi ne a dauki matakin da ya kamata a kan matasan duba da yadda su ka yi barazanar kashe su a cikin daren ranar karamar Sallah.

Biyu daga cikin matasan da ake zargi da yunkurin kashe 'yan bijilanten masu suna Shu'aibu Muhammad, da Abdulkadir Abubakar, sun ce kwayar da suka sha a cikin shayi ne suka tunzura su yunkurin kisan, amma sun yi nadama ba za su kara ba.

Daga bisani dai kakakin rundunar tsaron ta Anti-Phone Snaching Force da ke Kano, Ibrahim Garba Ahmad, ya ce tuni kwamandan rundunar Nura Salisu Sharada, ya bayar da umarnin a mika matasan inda ya dace domin daukar mataki na gaba.

Ya kuma gargaɗi dukkan matasan da ke da irin wannan ɗabi'ar da su guji hakan kasancewar rundunar na za ta saurara wa dukkanin wanda ya faɗa komar su ba.

Ready to PlayDala FM88.5 FM