Koma Labarai
Shari'a

Kotu ta aikewa Malam Lawan Triumph sammaci kan zargin kalaman tunzurawa al'umma a Kano.

Hassan Mamuda Ya'u 0 views
Kotu ta aikewa Malam Lawan Triumph sammaci kan zargin kalaman tunzurawa al'umma a Kano.

Babbar Kotun Shari’ar Musulunci da ke Ƙofar Kudu a jihar Kano, ta aikewa Malam Lawan Triumph sammaci domin ya bayyana a gabanta.

Kotun, ƙarƙashin jagorancin Alƙali Ibrahim Sarki Yola, ta bayar da sammacin ne bayan ƙarar da wasu ƙungiyoyin addinin Musulunci suka shigar a gaban ta.

Ƙungiyoyin, ƙarƙashin jagorancin Muhammad Al-Bakary Mika'il, suna zargin Malam Lawan Triumph da yin kalaman da ka iya tunzura al’umma.

Ana sa ran wanda ake ƙara zai bayyana a gaban kotun domin amsa ƙarar da aka shigar a kansa.

Ready to PlayDala FM88.5 FM