Kotu ta yi watsi da rokon mataimakin gwamnan Kano a kan batun tsige shi daga muƙamunsa
Hassan Mamuda Ya'u 0 views

Babbar kotun tarayya mai zaman ta a Kano, ta yi watsi da roƙon mataimakin gwamnan Jano Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, wanda ya roki kotun da takaddar kan tattauna batun tsige shi daga muƙamunsa.
Mai shari'a M S Shu'aibu ya ayyana cewar, mai ƙarar bai cika sharuɗan da shari'a aka tanadar ba a don haka ne aka yi watsi da roƙon.
Majalisar dokokin jahar Kano ce dai ta fara tattauna batun tsige mataimakin gwamnan a kwanakin baya, har ma ta bashi wa'adin mako biyu domin ya je ya kare kansa kan wasu korafe-korafe da aka yi a kansa.
Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma'il ya ruwaito cewa, kotun ta kuma ayyana cewar mai ƙara zai iya gabatar da takaddun kariya a gaban kwamitin binciken idan buƙatar hakan ta taso.



