Koma Labarai
Shari'a

Kotu ta yi watsi da rokon mataimakin gwamnan Kano a kan batun tsige shi daga muƙamunsa

Hassan Mamuda Ya'u 0 views
Kotu ta yi watsi da rokon mataimakin gwamnan Kano a kan batun tsige shi daga muƙamunsa

Babbar kotun tarayya mai zaman ta a Kano, ta yi watsi da roƙon mataimakin gwamnan Jano Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, wanda ya roki kotun da takaddar kan tattauna batun tsige shi daga muƙamunsa.

Mai shari'a M S Shu'aibu ya ayyana cewar, mai ƙarar bai cika sharuɗan da shari'a aka tanadar ba a don haka ne aka yi watsi da roƙon.

Majalisar dokokin jahar Kano ce dai ta fara tattauna batun tsige mataimakin gwamnan a kwanakin baya, har ma ta bashi wa'adin mako biyu domin ya je ya kare kansa kan wasu korafe-korafe da aka yi a kansa.

Wakilinmu Yusuf Nadabo Isma'il ya ruwaito cewa, kotun ta kuma ayyana cewar mai ƙara zai iya gabatar da takaddun kariya a gaban kwamitin binciken idan buƙatar hakan ta taso.

Ready to PlayDala FM88.5 FM