Connect with us

Manyan Labarai

Abin takaici ne yadda wasu jihohi har yanzu su ka gaza biyan ma’aikata sabon albashi – PRP

Published

on

Jam’iyyar hamayya ta PRP a Najeriya, ta yi Allah wa-dai da yadda har kawo yanzu wasu jihohi a ƙasar suka gaza fara biyan ma’aikatan jahohin su mafi ƙarancin albashi, duk kuwa da cire tallafin man fetur da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi, ya jefa rayuwar al’umma cikin ƙuncin rayuwa.

Hakan na ƙunshe ne ta cikin saƙon sabuwar shekara mai ɗauke da sa hannun mataimakin shugaban Jam’iyyar PRP na Arewa maso Yammacin ƙasa Abba Sule Namatazu, ya fitar ga manema labarai a ƙarshen makon nan.

“Jam’iyyar mu tana sane da shirin gwamnatin Tarayya na mayar da wasu makarantu Gwamnati masu zaman kansu da hakan ka iya tilastawa matasa da dama barin Makaranta, inda wasu ka iya fadawa cikin halin aikata laifuka, baya ga yadda rashin tsaro ke kara ta’azzara zuwa sassan Najeriya, “in ji Namatazu”.

Har ila yau, jam”iyyar hamayya ta PRP, ta nuna takaicinta kan yadda har yanzu Najeriya ba ta samu wani ci gaban azo-a-gani ba cikin shekara 64 da samun ‘Yancin kai, da kuma shekara 25 na mulkin Demukuraɗiyya ba tare da katsewa ba.

Namatazu, ya kuma ce bisa la’akari da shekarun da aka shafe da samun ƴancin kai, kamata ya yi ace ƙasar nan ta fita daga cikin ƙasashen da ke fama da talauci da rashin tsaro da cin hanci da rashawa, Sai dai hakan bata sami ba saboda rashin Ingantaccen shugabanci a cikin shekaru 25 daga 1999 zuwa yanzu.

Abba Namatazu ya kuma yi kira ga Gwamnatoci a kowane mataki da su ƙara ƙaimi wajen inganta fannnin aikin Gona, da lafiya, da Ilimi, da kuma Tsaro da sauraran fannonin ci gaban Al’umma.

Jam’iyyar ta PRP ta kuma bukaci ‘Yan Najeriya da su tabbatar da Kyakkyawan Shugabanci da kuma bibiyar shugabannin su.

Manyan Labarai

Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da duk wanda ya take haƙƙin mutane a Nijeriya – Human Rights

Published

on

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Sustainable Growth initiatives for Human Rights Development, ta ce babu ɗaga ƙafa a tsakanin ta da dukkanin wanda ya take wa wasu haƙƙi a Nijeriya, tana mai cewa za ta yi duk mai yiyuwa don ganin an dawo wa da dukkan wanda aka cuta haƙƙinsa.

Daraktan ƙungiyar na ƙasa Kwamared Abubakar Musa Abdullahi, ne ya bayyana hakan yayin zantwar sa da gidan rediyon Dala FM Kano, jim kaɗan bayan da su ka buɗe sabon ofishin ƙungiyar reshen unguwar Ƴanshana da ke ƙaramar hukumar Kumbotso, ranar Lahadi 09 ga watan Nuwamba, 2025, a Kano

Kwamared Abubakar, ya kuma ce za su ci gaba da hoɓɓasa wajen ganin sun ci gaba da bibiya akan cutar da aka yi wa mutane, don ganin an ƙwato musu haƙƙoƙin da aka danne musu ba tare da gajiya wa ba.

A cewar sa, “Daga cikin kuɗirin mu har da nema wa Matasa ayyukan yi, don yaƙi da rikice-rikicen faɗan Daba, da ƙwacen Wayoyi, da kuma daƙile shaye-shayen kayan maye a tsakanin al’umma, tare da taimakon marayu, don inganta rayuwar su, in ji Abubakar.”

Da yake nasa jawabin, sabon shugaban ƙungiyar ta Sustainable Growth initiatives for Human Rights and Development, reshen unguwar Ƴanshana da ke ƙaramar hukumar Kumbotso a Kano, Kwamared Yunusa Muhammad Ahmad, ya ce a shirye su ke wajen ci gaba da bibiya tare da kare haƙƙin bil’adama.

A yayin taron, an ƙaddamar da shugabannin da za su jagorancin aikin ƙungiyar na sabon ofishin da aka buɗe, wanda Kwamared Yunusa Muhammad Ahmad, zai jagorance su.

Taron ya samu halartar al’umma da dama, kuma ciki har da limamin masallacin unguwar Ƴanshana Mallam Muhktar, da mai unguwar yankin, da kuma kwamandan ƙungiyar sintirin Bijilante na unguwar, da dai sauransu.

Continue Reading

Manyan Labarai

Kotu ta sanya ranar yanke wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu hukunci

Published

on

Yanzu haka Babbar kotun Tarayya da ke birnin Abuja, ta saka ranar 20 ga watan Nuwamban 2025, domin yanke wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu hukunci akan tuhumar da ake yi masa.

Mai shari’a, a kotun, James Omotosho, ne ya bayyana haka a zaman kotun na ranar Juma’a 07 ga watan Nuwamba, 2025, a kan shari’ar da ake yi wa Kanu kan zargin ta’addanci.

Maishari’a James, ya ɗauki matakin ne bayan da Nnamdi Kanu, ya kasa fara kare kansa bayan kwana shida da kotun ta ba shi domin yin hakan, kamar yadda kafar BBC ta ruwaito.

Har ila yau, kotun ta kuma ce bayan Kanu ya gaza amfani da damar da aka ba shi domin kare kansa daga tuhumar da ake yi amsa, bai kamata ya ci gaba da iƙirarin da yake yi cewa an hana damar da kundin tsarin mulki ya ba shi na jin bahasinsa.

Idan ba a manta ba, a ranar 27 ga watan Oktoban da ya gabata ne dai, kotun ta ɗage zamanta domin bai wa wanda ake ƙara damar kare kansa kamar yadda ya buƙata a baya, sai dai a yanzu ya kasa kare kan nasa.

Continue Reading

Manyan Labarai

Kotu ta yanke wa magidanci hukuncin sharar Masallaci na tsawon wata 6 a Kano

Published

on

Kotun shari’ar Musulunci mai lamba daya da ke zamanta a Kofar Kudu, ta yanke wa wani magidanci hukuncin share Masallacin Wudilawa na tsawon wata shida bayan samun sa da laifin dukan matarsa.

Tunda fari, matar ta garzaya Ofishin ‘yan sanda ne da ke Jakara a Kano, inda ta yi ƙarar mijinta cewar ya doka mata Muciya a kanta sakamakon haka har sai da ta yi jinya.

Bayan Jin korafinta ne aka turasu Kotun Shari’ar Musulunci mai lamba daya da ke Kofar Kudu karkashin jagorancin mai sharia Shamsuddin Ado Abdullahi Unguwar Gini.

An kuma gurfanar da shi a kotun, bisa tuhumar samar da rauni, kuma bayan karanto masa ya amsa laifinsa, amma lauyansa wato daya daga cikin lauyan taimakon marasa ƙarfi Barista Muhammad Ali Tijjani, ya roƙi ayi masa sassauci.

Hakan ya sa kotu ta amince, ta kuma yanke masa hukuncin ɗaurin talala, inda zai share masallacin Wudilawa na tsawon watanni shida a sati sau uku.

Haka kuma, an tsalala masa bulala goma, kuma an umarcr shi da ya biya matar kudin maganin da ta kashe wato Naira dubu goma, kamar yadda Freedom Radio ta ruwaito.

Continue Reading

Trending