Connect with us

Labarai

WANI MASANIN HALAYYAR DAN ADAM DAKE KWALEJIN ILIMI A NAN KANO YA BAYYANA SON ABIN DUNIYA A MATSAYIN ABIN DA KE TAYA TABARBAREWAR HARKAR KOYARWA A KASAR NAN

Published

on

Wani Masanin Halayyar Dan Adam dake kwalejin Ilimi ta Tarayya a nan Kano Dakta Yunusa Kadiri ya bayyana son abin duniya a matsayin abin da ke taka rawa wajen tabarbarewar harkar koyarawa a kasar nan.

Dakta Yunusa Kadiri ya bayyana hakan ne yayin tattaaunarwa da wakilin mu Buhari Isah a ofishin sa a jiya litinin.

Ya ce, “kwadayi ne ya rufewa al’umma idanu a yanzu, a don haka mafi yawancin mutane a wannan lokacin basa son har kar koyarwa.”

Dr Yunusa Kadiri ya kara da cewa, “sai Gwamnati ta mutunta koyarwa sannan al’umma za su dauketa da muhimmanci.”

Dr Yunusa Kadiri ya kuma ja hankalin matasa da su rungumi harakar koyarwa don tallafawa harkar ilimi a kasar nan.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending