Labarai
An gargadi gwamnatin Kano kan kafa masarautu hudu

Ofishin lauyoyi dake nan Kano ya nemi gwanan Kano Abdullahi Umar Ganduje da majalisar dokoki wanda Abdul’aziz Garba Gafasa ke jagoranta da su jingine batun zartar dako sake gyaran dokar kafa rusassun masarautu hudu.
Masarautun sun hada da Bichi, Karaye, Gaya, da Rano bayan da justice Usman Na abba na babbar kotun jaha ya rushe makonni biyu da suka suka wuce.
Idan za’a iya tunawa Ofishin lauyoyin dai suke wakiltar madakin Kano da mutum uku a kunshin Sharia mai lamba K/ 197/2019 wadda take gaban babbar kotun jaha mai lamba uku karkashin Justice Ahmad Tijjani.
Sarki daya ne yanzu a Kano –Barista Danbaito
Raba Masarautar Kano: Umarnin kotu baizo mana akan lokaci ba -Sakataren gwamnatin Kano
Kurunkus: Ganduje ya rattaba hannu kan kudurin rarraba masarautar Kano
A Cikin kunshin kara da masarautar Kano ta shigar sun hada da shugaban majalisa da baturen Sharia da gwamnatin kano da kuma babban baturen Sharia.
Buga da kari, wakilin tashar Dala FM Yusuf Nadabo Isma’il ya rawaito cewa, ofishin lauyoyin sun bukaci a jingine wannan batu na gyaran dokar kirkirar masarautu tunda dai maganar da take gaban kotu kowa tsayawa yake ya jira hukuncin kotu

Baba Suda
Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.
Cikakken labarin na Zuwa….

Baba Suda
Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.
Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.
Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

Baba Suda
NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.
Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.
A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.
Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su