Connect with us

Manyan Labarai

Masarautar jihar kano ta koma kotu.

Published

on

Wasu lauyoyi anan karkashin jagorancin Barrister Abubakar Balarabe mahmud sun shigar da kudiri gaban babbar kotun jiha mai lamba 3.

kudirin nasu ya dogara da tanadi na 38/1, da kuma tanadi na 39 wanda ya kafa babbar kotun jiha ya kuma bata hurumin sauraron sauraron wannan roko.

Shariar mai kunshe da lamba k/197/2019
Wadda Yusuf Nabahani madakin kano, da Abdullahi sarki makaman kano, da Bello Abubakar sarkin Dawaki mai tuta da muktar Adnan sarkin Ban Kano suka shigar, suna karar gwamnan kano da shugaban majalisar dokokin kano da majalisar dokokin jihar da babban baturen Sharia da Tafida Abubuakr Ila da Ibrahim Abdulkadir Gaya da Dr Ibrahim Abubakar da Aminu Ado Bayero.

Rukon da masu kara sukayi Sun bukaci kotun da ta dakatar da wanda ake kara na 1 da na 2 da na 2 da na 4 ko dai su da kansu, ko kuma yan Korensu, su dakata daga yin wata doka ko ci gaba da ita ko tursasawa ko ci gaba da tursawa akan dokar tsaga masarauta.

Lauyoyin a madadin masu kara suna rokon a dakata har zuwa kammala shari’ar.

A sadara ta biyu cikin rokon Sun bukaci dakatar da wadanda ake kara na 1 zuwa na 4 ko su da kansu, ko yan korensu, ko hadiman su da su daina ayyana wadanda ake kara na 5 da 6 da na 7 da na 8 a matayin da dokar ta ayyanasu har zuwa karshen shari ar.

Sadara ta uku sun roki na 5 zuwa na 8 ko dai su da kansu ko yan korensu ko hadimansu da su daina bayyanasu a matasiyin sarakuna tunda dokar da ta kirkiresu ita ce kano state 2019 wadda wannan maganar dama tun tuni tana gaban wannan kotu mai girma a jira kuma jin ra ayin kotun.

Sadara ta 4 Sun roki kotun ta dakatar da gwamna daga daukar duk wani mataki ko canzawa sarkin Kano wata masarauta 8.

Sadara 6 lauyoyin Sun roki a dakatar da shugaban majalisar sarakuna ko shi da kansa ko yan korensa ko hadimansa daga shiga duk wata tattaunawa ta waccan da waccan doka ta tanada tun har zuwa karshen shariar.

Sai kuma sadarar da ta roki a dakatar da gwamna daka bikin nada sarakunan da waccan doka ta tanado tun da maganar tana gaban kotu.

Wakilin mu a kotu Yusuf Nadabo Ismail ya ruwaito cewa kotun ta sanya ranar 17 ga wannan watan domin fara sauraron wannan kudiri.

Idan dai zaa iya tunawa a makon daya gabata ne majalisar dokokin jihar kano ta amince da sabuqar dokar kafa masarautu 4 karkashin sarakunan yanka, bayan da kotu ta haramta irin wannan yunkuri a cikin watan 11 na shekarar dake bankwana.

Manyan Labarai

Bidiyon da ke yawo an sokawa wani matashi Wuƙa a ciki a Ɗorayi ba gaskiya ba ne – Cewar ƴan sandan Kano

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta umarci baturan ƴan sanda a faɗin jihar Kano, da su riƙe duk wanda yazo karɓar belin ƴan fashi da makamin da ta kama na yankin Ɗorayi ƙarama.

Kwamishinan ƴan sandan jihar Kano Muhammad Usaini Gumele, ne ya bayyana hakan yayin taron magance matsalar daba dake faruwa a unguwar Dorayi Karama, da ya gudana da yammacin yau Alhamis.

Rundunar ƴan sandan ta jihar Kano ta kuma musanta wani bidiyo dake yawo a shafukan sada zumunta dake nuna cewar ana cakawa wani matashi wuka a unguwar ta Dorayi Karama, wanda ta ce bidiyon ba gaskiya bane.

A nasa jawabin kwamnadan bijilanti na jihar Kano Shehu Muhammad Rabi’u, cewa ya yi masu bibiyar waɗanda aka kama da zargin aikata laifuka kamin kammala bincike na cikin dalilin karuwar matsalar daba da fashi da makami a lokuta da dama.

Da yake nasa jawabin dagacin Dorayi Karama Shehu Umar Sani, ya ce za su bayar da duk wani hadin kai da rundunar ƴan sandan take buƙata wajen kamo duk wanda yake cikin ƴan daba ko fashi da makami.

Rundunar ƴan sandan ta kuma ƙara da cewa za ta fara aikin kota kwana a yankin na Ɗorayi, tare da neman haɗin kan sauran jami’an tsaro dan tabbatar da tsare rayuka da dukiyoyin al’ummar yankin da ma na jihar Kano baki ɗaya.

A ƴan tsakanin nan ne dai wasu rukunin matasa suka addabi al’ummar yankin na Ɗorayi, inda aka zargi sun yi kan mai uwa dawabi akan mutane da sara, tare da ƙwacen wayoyin al’umma, bayyana da aka ce sun rarraba takardu kan cewar za su kai harin tare da hana yin sallar Tarawi.

Continue Reading

Manyan Labarai

DPO’s ɗin mu duk wanda ya zo belin ƴan Daba ku riƙeshi – Kwamishinan ƴan sandan Kano.

Published

on

Rundunar ƴan sandan Kano ta ce ta samar da rundunar yaƙi da ƴan Daba da ƴan Fashi da makamai, da suke addabar mutane a unguwar Ɗorayi ƙarama, tare da samar da gwangwanin Barkonon tsohuwa guda dubu ɗaya dan fara kakkaɓe ƴan Daba a yankin.

Kwamishinan ƴan sandan jihar CP Muhammad Usaini Gumel, ne ya bayyana hakan yayin wani taro na musamman da suka gudanar da masu ruwa da tsaki na unguwar Ɗorayi, da ya gudana yau a yankin wanda Kwamishinan ya jagoranta, domin lalubo hanyoyin magance matsalar tsaro a yankin.

CP Gumel, ya kuma umarci baturan ƴan sanda a faɗin jihar Kano, da su riƙe duk wanda yazo karɓar belin ƴan fashi da makamin da ta kama, kamar yadda wakilinmu Abba Isah Muhammad ya rawaito.

A ƴan tsakanin nan ne dai wasu rukunin matasa suka addabi al’ummar yankin na Ɗorayi, inda aka zargi sun yi kan mai uwa dawabi akan mutane da sara, tare da ƙwacen wayoyin al’umma, bayyana da aka ce sun rarraba takardu kan cewar za su kai harin tare da hana yin sallar Tarawi.

Continue Reading

Manyan Labarai

Mun sami karamar hukumar birni a cikin mawuyacin hali:Hon Bashir Chilla

Published

on

Shugabancin ƙaramar hukumar Birni na riƙo dake nan jihar Kano ya ce bayan karɓa wannan ƙaramar hukumar sun same ta cikin muhuyacin hali, kasancewar yadda sakatariyar take babu gyara babu kuɗi.

Shugaban karamar hukumar na riƙo Hon Bashir Baba Chilla ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a wani ɓangare na samarwa da ƙaramar hukumar Birni ci gaba.

Chilla ya kara da cewa sun sanya idanu kan ma’aikatan da suke aiki a wajen domin zuwa aiki akan lokaci da kuma gudanar da aiki yadda aka tanada domin sauke hakkin al’umma.

Akwai matsalar huta da wannan sakatariyar take fuskanta ta yadda a kullum takan zama babu huta sakamakon rashin kula da injin da yake bayar da huta,amma kawo wannan lokacin an samu gyara shi, inda yanzu haka huta ta samu a cikin sakatariyar, A cewar Chilla.

Akwai matsalar ƴan kilisa da wannan ƙaramar hukumar take fuskanta, adon haka ya zama wajibi shugabancin ƙaramar hukumar ya dau mataki domin kawo ƙarshen wannan ɓarna da ake yi a yayin hawan kilisar.

Haka kuma muna so musamar da kyakkyawan tsaro a ƙaramar hukumar shiyasa yanzu haka muka kafa wani kwamiti wanda zan sanya idon ko ta kwana musamman a wannan lokaci na ƙaratowar sallah karama.

Muna kira ga iyaye da su sanya idanu kan ƴaƴan su domin kaucewa rikice rikice da ake samu na yau da kullum a wannan ƙaramar hukumar.

Zamu tabbatar mun sanya idanu kan asibitocin mu da suke ƙaramar hukumar Birni domin bayar da kulawar lafiya ga dukkanin al’ummar da suke yankin ƙaramar hukumar.

Akwai tsarin da ƙaramar hukumar Birni tayi wajen bayar da tallafin abinci ga al’ummar ƙaramar hukumar ƙarkashin jagorancin gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf domin rage matsin rayuwa da al’umma suke ciki.

Hon Bashir Baba Chilla ya ce a wannan lokaci Ramadan an sami matsalar ciyarwa a wata santa da take ƙarƙashin sa wanda hakan baiyi daɗi ba kuma cikin ƙanƙanin lokaci aka sami canji, domin gudanar da abin da gwamnati ta tsara.

Ina kira ga al’umma duk abin da zasuyi su kasance sunyi abin su tsakanin su da Allah domin hakki ne da aka ɗorawa mu ku.

Domin wannan tsarin na ciyarwa a buƙatar ya isa ga kowa da kowa musamman bamuƙata da suke faɗin jihar nan.

Continue Reading

Trending