Connect with us

Labarai

Harkar lafiya za ta inganta matukar gwamnati za ta tallafa

Published

on

Dagacin Kabo Malam Auwalu Zubairu,ya bukaci wandanda suka amfana da aikin duba lafiya kyauta, su bi ka’idar yadda aka basu magani tare da neman wanda aka rubuta musu.

Malam Auwalu Zubairu Kabo, ya bayyana hakan lokacin da daliban sashin koyon aikin jinya dake Jami’ar Bayero a jihar Kano suka ziyarci karamar hukumar Kabo don duba mutane tare da basu magani kyauta a wani bangare na baiwa al’umma gudummawa.

Dagacin wanda Alhasan Hamisu Kabo, ya wakilta ya kara da cewar za a samu ingantuwar harkokin lafiya matukar kungiyoyi da gwamnati za su waiwayi mazauna karkara a fannin lafiya don tallafa musu.

A nasa jawabin kwamishinan lafiya na karamar hukumar ta Kabo, Murtala Ahmad Masanawa, cewa yayi karamar hukumar Kabo na bakin kokarinta a fannin inganta harkokin lafiya ta hanyar tsarin kota kwana.

Da yake jawabi tunda farko shugaban kungiyar dalibai masu karatun aikin jinya reshen jami’ar Bayero Kano, Salman Nafiu Abbas, ya bayana cewar duba lafiyar wani bangare ne na taron da suka saba gudanarwa duk shekara.

Wanda a bana ya maida hankali kan fito da illolin masu shiga aikin jniya ba tare da ilimi ba, da kuma abinda yake haifarwa tare da yadda za’a magancesu.

Wakilinmu Abba Isah Muhammad, ya ruwaito cewar wadanda suka amfana da aikin duba lafiyar sun hadar da mata da maza wanda kuma suka bayyana farin cikin su tare da godewa kungiyar daliban.

Labarai

NAHCON ta sanya ranar fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa Saudiyya

Published

on

Yanzu haka hukumar Aikin Hajji ta ƙasa NAHCON, ta 15 ga watan nan na Mayun 2024, a matsayin ranar da za’a fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana, zuwa ƙasa mai tsarki.

Bayanin hakan ya fito ne ta bakin shugaban hukumar ta NAHCON, Jalal Ahmad Arabi, a wajen taron masu ruwa da tsaki kan aikin Hajji da Umrah, da ya gudana yau Alhamis birnin tarayya Abuja.

“Maniyyata kimanin 65,500 ne za su sauke Farali daga ƙasar nan a ƙasa mai tsarki; za su shafe aƙalla kwanaki huɗu domin yin ziyara a Madina kafin fara aikin Hajji, “in ji Arabi”.

Daga bisani shugaban hukumar aikin hajjin Jalal Ahmad Arabi, ya kuma bayyana cewa za ayi jigilar maniyyata aikin hajjin ne daga cibiyoyi 10 a faɗi ƙasar nan.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin ranar hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Talata.

Olubunmi, ya kuma sake nanata buƙatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkanib matakai daban-daban.

Continue Reading

Labarai

Wahalar Fetur ta haifar mana da koma baya a sana’ar mu – Mai Motar Haya

Published

on

Wani mai sana’ar tuƙin motar Haya, da kuma lodin fasinjoji mai suna Kabiru Muhammad, mazaunin ƙaramar hukumar Munjibir, ya ce ƙarancin motocin Haya da ake samu a yanzu, yana da alaƙa da wahalar man Fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya.

A zantawar mutumin da wakilinmu Yusuf Nadabo Isma’il, ta cikin shirin rahotanni daga ƴan Zazu na yau Talata, ya ce a baya har motoci hamsin suke yiwa lodin fasinjoji su tashi, amma a yanzu Mota ɗaya suke iya cikawa sakamakon ƙarancin Fetur da ake fama da shi.

Ya kuma ce ƙaranci tare da tsadar man fetur ɗin da ake fama da shi, sun haddasa musu koma baya a sana’ar su, baya ga batun kuma matsalar da suke fuskanta da fasinjoji wajen biyan kuɗin Mota.

Wakiliyarmu da ta bibiyi shirin na ƴan Zazu Ummi Bala Ahmad ta rawaito cewa, matuƙin motar Kabiru Muhammad, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jahohi, da su yi abinda ya kamata dan ganin farashin man Fetur ɗin ya sauka, domin al’umma su samun sauƙi.

Continue Reading

Trending