Connect with us

Labarai

GWAMNATIN JIHAR NEJA TA KAI ZIYARA KAUYEN RAFINGORA.

Published

on

Gwamnatin jihar Naija ta kai ziyara kauyen Rafingora dake karamar Hukumar Kontagora a jihar, sakamakon anbaliyar ruwa da ta faru a yankin wanda yayi sanaddiyar mutuwa mutane 10 tare da rushe gidaje sama da 300.

A makon da ya gabata ne dai Hukumonin jihar Naija suka tabbatar da mutuwar wasu matasa 10 tara da yin awon gaba da gidajen jama’a kimanin 300 a kauyen Rafingora dake karamar Hukumar kontagora.

Gwamnan jihar Alhaji Abubakar Sani Bello ya ce, “har yanzu mutanen garin na cikin hadari bisa la’akari da abinda ya gani, don haka zasu nemi tallafin gwamnatin tarayya domin tabbatar da an canza wa mutanen garin matsugunni.”

Gwamnan ya kara da cewa, “mazaunan garin suna cikin wani yanayi na tashin hankali a sakamakon hasarar matsugunan su da kayayyakin abinci, a don haka suka dauki gabaren sauyawa wadanda suka rage matsuguni don gudun kada anbaliyar ruwan ta shafe su.”

A halin yanzu Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar na ci gaba da tattara bayanai domin tantance asarar da ambaliyar ruwan ta haddasa kamar yadda shugaban hukumar Alhaji Ibrahim Inga ya tabbatar.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending