Labarai
OFISHIN JAKADANCIN AMURKA A NAJERIYA YA BUKACI GWAMNONIN JIHOHIN KASAR NAN SU KARFAFA MATAKAN TSARO A FADIN KASAR
Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya, ya bukaci gwamnonin jihohin kasar nan da su karfafa matakan tsaro musamman jami’an ‘yan sanda wajen basu horo da kayan aiki domin samar da ingantaccen tsaro a fadin kasar nan.
Hakan ya fitone ta bakin Mataimakin shugaban ofishin jakadancin Amurka a Nigeria David Young, a yayin wata ziyara da yakai jihar Plateau, don jajantawa al’ummar jihar akan rikicin da ya faru a Barikin Ladi.
A yayin ziyarar tasa David Young, ya nuna takaicinsa ga irin barnar da rikicin ya haifar, inda ya kira ga gwamnati da ta dauki matakan kawo karshen tashe tashen hankali a kasar nan.
Mr. David Young ya ce ya kai ziyarar ne domin ya fahimci abun dake faruwa, ta yadda za’a hada karfi da karfe wajen hana sake aukuwar lamarin anan gaba. Ya ce “kamata yayi a taimakawa wadanda rikicin ya rutsa dasu, tare da samar da sabbin tsaren tsaren tabbatar da zaman lafiya a yankin.”
Mr Young ya kara da cewa “yakamata Nigeria ta tashi tsaye wajen aiwatar da doka, ta hanyar samar da ‘yan sanda da horas dasu tare da basu kayan aiki da kuma albashin su, domin su gudanar da ayyukansu na tsaron lafiyar mutane da dukiyoyinsu.”

Baba Suda
Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.
Cikakken labarin na Zuwa….

Baba Suda
Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.
Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.
Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

Baba Suda
NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.
Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.
A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.
Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

-
Nishadi6 years ago
Ina neman mijin aure – Rayya
-
Labarai5 years ago
Hamisu Breaker ya kai kan sa wajen ‘yan sanda
-
Nishadi6 years ago
Mansura Isah ta yi kaca-kaca da Sadiya Haruna
-
Manyan Labarai5 years ago
KAROTA: An baiwa Baffa Babba wa’adin kwanaki bakwai
-
Labarai5 years ago
Auren dan Panshekara da ba Amurkiya ya samu cikas
-
Lafiya3 years ago
Rahoto: An gano wani gida da ake gini da takardun Kur’ani da Alluna
-
Manyan Labarai5 years ago
Sabuwar damfarar da ta fito a Kano
-
Nishadi6 years ago
An gano daliban da Adam Zango ya dauki nauyin karatun su