Connect with us

Labarai

Jirgin dakon kaya na farko ya fara sauka a tashar ruwan Lekki – Buhari

Published

on

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya taya ma’aikatar sufuri ta tarayya da hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa ta kasa, murna kan nasarar da aka samu na jigilar jirgin ruwa na farko a tashar ruwan Lekki Deep Sea da ke jihar Legas.

Jirgin mai suna ZHEN HUA 28, ya kai jirgin ruwa guda uku zuwa teku da wasu kugiya guda 10,  wadanda za su taimaka wajen fitar da kayayyaki daga tasoshin zuwa gaci.

Shugaban ya bayyana ra’ayinsa ne a wata sanarwa da mai magana da yawunsa Femi Adesina ya fitar ranar Asabar a Abuja.

Ya kuma taya dukkan masu ruwa da tsaki a harkar ruwa murnar wannan gagarumin aiki.

A cewarsa, an yanke shawarar ne da nufin samar da guraben ayyukan yi masu tarin yawa, zuba jarin kasashen waje da kuma saukaka harkokin kasuwanci.

Ya yabawa ma’aikata da masu gudanarwa a bangaren ruwa na kasar da suke aiki ba dare ba rana don ganin an fara gudanar da aikin tashar ruwan Lekki kafin karshen shekara.

Shugaban ya tabbatar musu da kudirinsa na ci gaba da saka hannun jari a wadannan sabbin kadarorin.

A cewar Buhari, albarkatun ruwa da na ruwa na kasar na da matukar muhimmanci ga rayuwar ‘yan Najeriya kuma gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen samun nasarar cin moriyar wannan fanni.

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Labarai

Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta

Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.

 

Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.

Continue Reading

Daurin Boye

Zan shiga kawancen ‘yan jamiyyar hamayya – tsohon Minista

Published

on

Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan jamiyyar hamayya domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027

A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar.

Amaechi wanda ɗan jam’iyyar APC ne  ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira halin ƙuncin rayuwa da ƙasar ke ciki.

Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance.

Continue Reading

Trending