Connect with us

Labarai

Inganta tsarin kasa da kasa zai inganta harkokin lafiya – Atiku

Published

on

Dan takarar shugaban kasa a Jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya shawarci hukumar asibitin Nizamiye da su ingantaccen tsarin kasa da kasa bawai kawai iya kayan aiki ba.

Atiku ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi ayarin hukumar gudanarwar rukunin First Surat Group, karkashin manajan daraktan, Yeser Ovenc, inda suka ziyarce shi a gidan sa na Asokoro dake Abuja jiya Juma’a.

Sanarwar da mai taimaka masa na musamman a harkokin yada labarai, Abdulrasheed Shehu ya sanyawa hannu, Mr Servet Gulerman, ya godewa Wazirin Adamawa, saboda samun lokacin karbar tawagar ta su, inda ya ce, sun je ne musamman domin taya shi murnar lashe zaben fitar da gwani na PDP tare da yi masa fatan nasara a babban zabe na badi.

Haka kuma, sun godewa tsohon mataimakin shugaban kasar ta Najeriya saboda irin taimako da goyon bayan da ya rika bawa kamfanin a baya. Inda ya ce, a matsayin su na wakilan al’ummar Turkawa a Najeriya sun kaiwa Wazirin na Adamawa ziyarar ban girma, yana mai cewa, za su ci gaba da zuba hannayen jari da ayyuka da za su amfani kasashen biyu domin kyautata alakar su.

Ya ce, “Irin nasarar da suka samu da fadada kwarewa a Asibitin a fannin tiyata da ta shafi zuciya da sauran cututtukan zuciya da nasara Kashi 99 cikin dari, zai taimaka mutuka Wajen rage zuwa Asibitin kasashen Waje inda aka mori Asibitin yadda ya dace”.

Baba Suda

Hukumar tattara kudaden shiga ta Kano ta rufe wasu bankuna

Published

on

Hukumar Tattara kudaden shiga ta jahar kano ta kulle bakin Eco da Zenith dake kan titin Murtala Muhammad. Sakamakon rashin biyan haraji.

Cikakken labarin na Zuwa….

Continue Reading

Baba Suda

Kisan Makurdi:- Gwamnatin Kano za ta tura wakilai

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano tayi Allah wadai da kisan mutane biyu Yan Jihar a garin Makurdi dake Jihar Benue.

Cikin sanarwar da Daraktan Gwamnan Kano kan harkokin yada labarai Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ta ruwaito Gwamnan na Mika sakon jaje ga alummar Jihar da iyalai da ‘yan uwan wadanda abin ya rutsa dasu, Barhma Suleman da Jamilu Ahmad.

 

Kazalika Gwamnan yayi alkawarin daukar Matakin da ya dace kan batun, tare da fadin gwamnatin Kano za ta tashi wakilai har Zuwa Jihar Benue domin tabbatar da daukar Matakin da ya dace.

 

 

Continue Reading

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Trending