Connect with us

Labarai

Inganta tsarin kasa da kasa zai inganta harkokin lafiya – Atiku

Published

on

Dan takarar shugaban kasa a Jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya shawarci hukumar asibitin Nizamiye da su ingantaccen tsarin kasa da kasa bawai kawai iya kayan aiki ba.

Atiku ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi ayarin hukumar gudanarwar rukunin First Surat Group, karkashin manajan daraktan, Yeser Ovenc, inda suka ziyarce shi a gidan sa na Asokoro dake Abuja jiya Juma’a.

Sanarwar da mai taimaka masa na musamman a harkokin yada labarai, Abdulrasheed Shehu ya sanyawa hannu, Mr Servet Gulerman, ya godewa Wazirin Adamawa, saboda samun lokacin karbar tawagar ta su, inda ya ce, sun je ne musamman domin taya shi murnar lashe zaben fitar da gwani na PDP tare da yi masa fatan nasara a babban zabe na badi.

Haka kuma, sun godewa tsohon mataimakin shugaban kasar ta Najeriya saboda irin taimako da goyon bayan da ya rika bawa kamfanin a baya. Inda ya ce, a matsayin su na wakilan al’ummar Turkawa a Najeriya sun kaiwa Wazirin na Adamawa ziyarar ban girma, yana mai cewa, za su ci gaba da zuba hannayen jari da ayyuka da za su amfani kasashen biyu domin kyautata alakar su.

Ya ce, “Irin nasarar da suka samu da fadada kwarewa a Asibitin a fannin tiyata da ta shafi zuciya da sauran cututtukan zuciya da nasara Kashi 99 cikin dari, zai taimaka mutuka Wajen rage zuwa Asibitin kasashen Waje inda aka mori Asibitin yadda ya dace”.

Baba Suda

NNPP:- Kwankwaso ya sulhunta rikicin jamiyyar

Published

on

Rahotanni daga Abuja sun tabbatar da jagoran kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi wani zama da Dan majalisar tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Rimin Gado, Tofa da Dawakin Tofa, Wato Honorable Abdulkadir Jobe, da kuma Daraktan yada labaran Gwamnan Kano Honorable Sunusi Bature Dawakin Tofa.

 

Ganawar wadda ta gudana a yammacin wannan Alhamis ta kawo karshen Jan Zaren dake faruwa tsakanin Dan majalisar da kuma Sunusi Bature.

 

A baya bayan nan dai an kai ruwa rana tsakanin su, Inda kowa ne bangare ke mayar da martani.

Abdulkadir Jobe da kuma Sunusi Bature dukkanin su mabiya jamiyyar NNPP ne tsagin kwankwasiyya.

Continue Reading

Labarai

Real Madrid ta kaddamar da Alexander

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid ta ƙaddamar da ɗan wasa Trent Alexander Arnold a yau a matsayin ɗan wasan ta

Inda shugaban ƙungiyar Flerontino Perez yace yau suna matuƙar Farin ciki kasancewar sun mallaki babban ɗan wasan baya a duniya.

 

Shima ɗan Wasa Arnold ya bayyana cewa yana cikin farin ciki kuma mafarkin sa ya cika na zama ɗan Wasan Madrid a yau.

Continue Reading

Daurin Boye

Zan shiga kawancen ‘yan jamiyyar hamayya – tsohon Minista

Published

on

Tsohon ministan sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce a shirye yake don shiga ƙawancen ƴan jamiyyar hamayya domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027

A wata hira da BBC, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce suna ƙoƙarin samar da haɗakar siyasar da za ta samar da sauyi a ƙasar.

Amaechi wanda ɗan jam’iyyar APC ne  ya nuna damuwa kan abin da ya ƙira halin ƙuncin rayuwa da ƙasar ke ciki.

Amaechi ya ce bai cire tsammanin yin takarar shugaban ƙasa ba, illa lokaci ne kawai zai tantance.

Continue Reading

Trending